• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Ne Suka Tunzura Mutane Yin Zanga-zanga A Neja Da Kano – APC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyya mai mulki ta APC ta zargi ‘yan adawa daga wasu jam’iyya ne suka haddasa zanga-zanga a Neja da Kano a ranar Litinin kan tsadar rayuwa, domin a taba wannan gwamnati.

A cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na jam’iyyar, Felid Morka ya fitar ranar Talata a Abuja, ya zargi ‘yan adawa da shirya makarkashiya na tunzura mutane su yi zanga-zanga kan tsadar rayuwa wanda hakan zai raunata gwamnati.

  • Al’ummar Kano Na Mutuwa Da Yunwa Da Fatara – Gwamna Yusuf  
  • Tsadar Rayuwa: ‘Yansanda Sun Kama Mutane 25 Da Zargin Yin Zanga-zanga A  Minna

A ranar Litinin masu zanga-zanga sun rufe babban hanyar Bida da Kpakungun da ke garin Mina dauke da kwalayen da aka rubuta cewa, “Babu abinci, muna mutuwa saboda yunwa”, “A rage farashin man fetur”, A taimaka mana mu sami abinci cikin sauki.”

Haka zalika, wasu matasa a Jihar Kano sun gudanar da zanga-zanga a kan manyan hanyoyi kan tashin gworon zabi na kayayyakin abinci, musamman ma shinkafa, masara, wake da kuma dawa.

Morka ya bayyana cewa gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu za ta yi duk mai yuwuwa wajen ganin ta kawo sauye-sauye masu muhimmanci da za su taimaka na habaka tattalin arziki da kawo wa ‘yan Nijeriya saukin rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

Ya gargadi ‘yan Nijeriya su yi watsi da abin da ya kira kokarin tarwatsa kasa da ‘yan adawa ke kokarin yi saboda su cimma burikansu na siyasa.

A cewar mai magana da yawun APC, “Domin nuna yin bore ga gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta, ‘yan adawa sun yi amfani da matasa wurin sudanar da zanga-zanga a wasu manyan burane.

“Zanga-zangar da suka gudana a Neja da Kano shiryayye daga ‘yan adawa, wanda suka yi kokarin tunzura mutane su bujere wa gwamnati saboda tsabar son zuciya. Wannan yunkure ne na tayar da zaune tsaye da barazana ga zaman lafiyar jama’a da kuma kawo rashin tsaro a cikin kasa.

“Yayin da muke ganin hakkin ‘yan kasa ne su yi  zanga-zangar lumana, muna kira ga mutanenmu su kasance a ankare kuma ka da su ba da dama ga kokarin da ‘yan adawa suke yi wajen haddasa rikice-rikice.

“Gwamnatin Tinubu ta kafa kwamiti da zai duba hanyoyin sake inganta tattalin arziki da zai taimaka wa ‘yan Nijeriya. Ba tare da hadin kan ‘yan kasa ba wajen yin biyayya ga gwamnati, to shirin ba zai samu ba. A cikin kannanin lokaci, shirin zai sauya alkablar matsin rayuwar da ake ciki a kasar nan.

“Muna kira ga ‘yan Nijeriya da su guji kokarin da ‘yan adawa ke yi na tarwatsa kasa domin samun nasarar siyasa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hauhawar Farashisiyasar NijeriyaTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Murnar Bikin Bazara Na Kasar Sin Ya Haskaka Gasar Wasan Kwallon Gora Kan Kankara Ta Arewacin Amurka

Next Post

Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

Related

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 
Manyan Labarai

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

1 hour ago
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

13 hours ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

16 hours ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

17 hours ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

18 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

20 hours ago
Next Post
Ezekwesili

Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

LABARAI MASU NASABA

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.