• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Ne Suka Tunzura Mutane Yin Zanga-zanga A Neja Da Kano – APC

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyya mai mulki ta APC ta zargi ‘yan adawa daga wasu jam’iyya ne suka haddasa zanga-zanga a Neja da Kano a ranar Litinin kan tsadar rayuwa, domin a taba wannan gwamnati.

A cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na jam’iyyar, Felid Morka ya fitar ranar Talata a Abuja, ya zargi ‘yan adawa da shirya makarkashiya na tunzura mutane su yi zanga-zanga kan tsadar rayuwa wanda hakan zai raunata gwamnati.

  • Al’ummar Kano Na Mutuwa Da Yunwa Da Fatara – Gwamna Yusuf  
  • Tsadar Rayuwa: ‘Yansanda Sun Kama Mutane 25 Da Zargin Yin Zanga-zanga A  Minna

A ranar Litinin masu zanga-zanga sun rufe babban hanyar Bida da Kpakungun da ke garin Mina dauke da kwalayen da aka rubuta cewa, “Babu abinci, muna mutuwa saboda yunwa”, “A rage farashin man fetur”, A taimaka mana mu sami abinci cikin sauki.”

Haka zalika, wasu matasa a Jihar Kano sun gudanar da zanga-zanga a kan manyan hanyoyi kan tashin gworon zabi na kayayyakin abinci, musamman ma shinkafa, masara, wake da kuma dawa.

Morka ya bayyana cewa gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu za ta yi duk mai yuwuwa wajen ganin ta kawo sauye-sauye masu muhimmanci da za su taimaka na habaka tattalin arziki da kawo wa ‘yan Nijeriya saukin rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Ya gargadi ‘yan Nijeriya su yi watsi da abin da ya kira kokarin tarwatsa kasa da ‘yan adawa ke kokarin yi saboda su cimma burikansu na siyasa.

A cewar mai magana da yawun APC, “Domin nuna yin bore ga gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta, ‘yan adawa sun yi amfani da matasa wurin sudanar da zanga-zanga a wasu manyan burane.

“Zanga-zangar da suka gudana a Neja da Kano shiryayye daga ‘yan adawa, wanda suka yi kokarin tunzura mutane su bujere wa gwamnati saboda tsabar son zuciya. Wannan yunkure ne na tayar da zaune tsaye da barazana ga zaman lafiyar jama’a da kuma kawo rashin tsaro a cikin kasa.

“Yayin da muke ganin hakkin ‘yan kasa ne su yi  zanga-zangar lumana, muna kira ga mutanenmu su kasance a ankare kuma ka da su ba da dama ga kokarin da ‘yan adawa suke yi wajen haddasa rikice-rikice.

“Gwamnatin Tinubu ta kafa kwamiti da zai duba hanyoyin sake inganta tattalin arziki da zai taimaka wa ‘yan Nijeriya. Ba tare da hadin kan ‘yan kasa ba wajen yin biyayya ga gwamnati, to shirin ba zai samu ba. A cikin kannanin lokaci, shirin zai sauya alkablar matsin rayuwar da ake ciki a kasar nan.

“Muna kira ga ‘yan Nijeriya da su guji kokarin da ‘yan adawa ke yi na tarwatsa kasa domin samun nasarar siyasa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hauhawar Farashisiyasar NijeriyaTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Murnar Bikin Bazara Na Kasar Sin Ya Haskaka Gasar Wasan Kwallon Gora Kan Kankara Ta Arewacin Amurka

Next Post

Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

3 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

5 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

6 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

7 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

10 hours ago
Next Post
Ezekwesili

Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.