• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Ne Suka Tunzura Mutane Yin Zanga-zanga A Neja Da Kano – APC

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyya mai mulki ta APC ta zargi ‘yan adawa daga wasu jam’iyya ne suka haddasa zanga-zanga a Neja da Kano a ranar Litinin kan tsadar rayuwa, domin a taba wannan gwamnati.

A cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na jam’iyyar, Felid Morka ya fitar ranar Talata a Abuja, ya zargi ‘yan adawa da shirya makarkashiya na tunzura mutane su yi zanga-zanga kan tsadar rayuwa wanda hakan zai raunata gwamnati.

  • Al’ummar Kano Na Mutuwa Da Yunwa Da Fatara – Gwamna Yusuf  
  • Tsadar Rayuwa: ‘Yansanda Sun Kama Mutane 25 Da Zargin Yin Zanga-zanga A  Minna

A ranar Litinin masu zanga-zanga sun rufe babban hanyar Bida da Kpakungun da ke garin Mina dauke da kwalayen da aka rubuta cewa, “Babu abinci, muna mutuwa saboda yunwa”, “A rage farashin man fetur”, A taimaka mana mu sami abinci cikin sauki.”

Haka zalika, wasu matasa a Jihar Kano sun gudanar da zanga-zanga a kan manyan hanyoyi kan tashin gworon zabi na kayayyakin abinci, musamman ma shinkafa, masara, wake da kuma dawa.

Morka ya bayyana cewa gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu za ta yi duk mai yuwuwa wajen ganin ta kawo sauye-sauye masu muhimmanci da za su taimaka na habaka tattalin arziki da kawo wa ‘yan Nijeriya saukin rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Ya gargadi ‘yan Nijeriya su yi watsi da abin da ya kira kokarin tarwatsa kasa da ‘yan adawa ke kokarin yi saboda su cimma burikansu na siyasa.

A cewar mai magana da yawun APC, “Domin nuna yin bore ga gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta, ‘yan adawa sun yi amfani da matasa wurin sudanar da zanga-zanga a wasu manyan burane.

“Zanga-zangar da suka gudana a Neja da Kano shiryayye daga ‘yan adawa, wanda suka yi kokarin tunzura mutane su bujere wa gwamnati saboda tsabar son zuciya. Wannan yunkure ne na tayar da zaune tsaye da barazana ga zaman lafiyar jama’a da kuma kawo rashin tsaro a cikin kasa.

“Yayin da muke ganin hakkin ‘yan kasa ne su yi  zanga-zangar lumana, muna kira ga mutanenmu su kasance a ankare kuma ka da su ba da dama ga kokarin da ‘yan adawa suke yi wajen haddasa rikice-rikice.

“Gwamnatin Tinubu ta kafa kwamiti da zai duba hanyoyin sake inganta tattalin arziki da zai taimaka wa ‘yan Nijeriya. Ba tare da hadin kan ‘yan kasa ba wajen yin biyayya ga gwamnati, to shirin ba zai samu ba. A cikin kannanin lokaci, shirin zai sauya alkablar matsin rayuwar da ake ciki a kasar nan.

“Muna kira ga ‘yan Nijeriya da su guji kokarin da ‘yan adawa ke yi na tarwatsa kasa domin samun nasarar siyasa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hauhawar Farashisiyasar NijeriyaTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Murnar Bikin Bazara Na Kasar Sin Ya Haskaka Gasar Wasan Kwallon Gora Kan Kankara Ta Arewacin Amurka

Next Post

Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

4 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

5 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

6 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

8 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

13 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

14 hours ago
Next Post
Ezekwesili

Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.