• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Adawa Ne Suka Tunzura Mutane Yin Zanga-zanga A Neja Da Kano – APC

byYusuf Shuaibu
2 years ago
APC

Jam’iyya mai mulki ta APC ta zargi ‘yan adawa daga wasu jam’iyya ne suka haddasa zanga-zanga a Neja da Kano a ranar Litinin kan tsadar rayuwa, domin a taba wannan gwamnati.

A cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na jam’iyyar, Felid Morka ya fitar ranar Talata a Abuja, ya zargi ‘yan adawa da shirya makarkashiya na tunzura mutane su yi zanga-zanga kan tsadar rayuwa wanda hakan zai raunata gwamnati.

  • Al’ummar Kano Na Mutuwa Da Yunwa Da Fatara – Gwamna Yusuf  
  • Tsadar Rayuwa: ‘Yansanda Sun Kama Mutane 25 Da Zargin Yin Zanga-zanga A  Minna

A ranar Litinin masu zanga-zanga sun rufe babban hanyar Bida da Kpakungun da ke garin Mina dauke da kwalayen da aka rubuta cewa, “Babu abinci, muna mutuwa saboda yunwa”, “A rage farashin man fetur”, A taimaka mana mu sami abinci cikin sauki.”

Haka zalika, wasu matasa a Jihar Kano sun gudanar da zanga-zanga a kan manyan hanyoyi kan tashin gworon zabi na kayayyakin abinci, musamman ma shinkafa, masara, wake da kuma dawa.

Morka ya bayyana cewa gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu za ta yi duk mai yuwuwa wajen ganin ta kawo sauye-sauye masu muhimmanci da za su taimaka na habaka tattalin arziki da kawo wa ‘yan Nijeriya saukin rayuwa.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Ya gargadi ‘yan Nijeriya su yi watsi da abin da ya kira kokarin tarwatsa kasa da ‘yan adawa ke kokarin yi saboda su cimma burikansu na siyasa.

A cewar mai magana da yawun APC, “Domin nuna yin bore ga gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta, ‘yan adawa sun yi amfani da matasa wurin sudanar da zanga-zanga a wasu manyan burane.

“Zanga-zangar da suka gudana a Neja da Kano shiryayye daga ‘yan adawa, wanda suka yi kokarin tunzura mutane su bujere wa gwamnati saboda tsabar son zuciya. Wannan yunkure ne na tayar da zaune tsaye da barazana ga zaman lafiyar jama’a da kuma kawo rashin tsaro a cikin kasa.

“Yayin da muke ganin hakkin ‘yan kasa ne su yi  zanga-zangar lumana, muna kira ga mutanenmu su kasance a ankare kuma ka da su ba da dama ga kokarin da ‘yan adawa suke yi wajen haddasa rikice-rikice.

“Gwamnatin Tinubu ta kafa kwamiti da zai duba hanyoyin sake inganta tattalin arziki da zai taimaka wa ‘yan Nijeriya. Ba tare da hadin kan ‘yan kasa ba wajen yin biyayya ga gwamnati, to shirin ba zai samu ba. A cikin kannanin lokaci, shirin zai sauya alkablar matsin rayuwar da ake ciki a kasar nan.

“Muna kira ga ‘yan Nijeriya da su guji kokarin da ‘yan adawa ke yi na tarwatsa kasa domin samun nasarar siyasa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Ezekwesili

Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version