• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Afirka Da Za Su Haska A Firimiyar Ingila

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
10 months ago
in Wasanni
0
‘Yan Afirka Da Za Su Haska A Firimiyar Ingila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Juma’a 16 ga watan Agusta aka fara gasar firimiyar Ingila, gasar da ake ganin za ta iya samar da canji a bangaren kungiyar da za ta iya lashe gasar, bayan shafe kakar wasa hudu kungiyar Manchester City tana lashe gasar a jere.

A baya dai an yi zakakuran ‘yan wasa daga nahiyar Afirka da suka haska a gasar ta Ingila irinsu Didier Drogba da Yaya Taure da Yakubu Ayegbeni da Machael Essien da Nwanko Kanu da Jay-Jay Okocha da sauransu.

Sai dai kawo yanzu akwai da yawa daga cikin manyan ‘yan wasa daga Afirka da suke buga kwallo a gasar da suka hada da Mohammad Salah da Muhammad Kudus da Adingra da sauran ‘yan wasan da suke buga wasa a wannan kakar a Ingila.

 

Muhammad Salah

Labarai Masu Nasaba

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

Dan wasan kasar Masar, Mohamed Salah zai iya bugan kirjinsa ya ce shi ne kan gaba cikin ƴan kwallon Afirka da suka taba buga gasa a Gasar Firimiyar Ingila amma kuma yadda kyaftin din na tawagar Masar ke buga wasa, za a iya cewa kakar bara ba ta yi masa kyau ba, inda ita kanta kungiyar Liberpool ta gaza wajen yin katabus.

Kwallaye 18 da ya zura ne a kakar bara, biyar a bugun fanareti- shi ne adadi mafi kankanta da ya zura tun zuwansa kungiyar a shekarar 2017, duk da cewa ya taimaka an zura kwallo sau 10 sannan ciwo ya hana dan wasan mai shekara 32 buga Gasar Kofin Afirka ta 2023, da kuma wasu wasanni, sannan abubuwa sun kara cabewa a lokacin da aka hango shi yana musayar yawo da kocinsa na wancan lokacin, Jurgen Klopp.

Amma bayan Klopp ya bar Liberpool, da kuma kasancewar saura masa shekara 1 a kwantiraginsa, sai aka fara hasashen cewa Muhammad Salah zai bar Liberpool, har aka fara cewa zai koma Saudiyya da buga wasa.
Ana cikin wannan ne Salah ya sanar da cewa zai ci gaba da zama a Liberpool, inda ya ce zai fafata domin gyara abubuwan da suka faru da kungiyar a kakar bara, inda ta kare ba tare da lashe wani kofi ba. Sai dai kawo yanzu ba a sani ba ko zai ci gaba da kasancewa a kungiyar karkashin sabon kociyan kungiyar Arne Slot?

Yiwuwar sauya salon wasan kungiyar, daga yawan kai hare-hare, zuwa tsarin da ake kira da na ‘Dutch’ na (rarraba kwalo daga gida zuwa tsakiya, sannan a jefa wa dan wasan gaba) watakila zai iya yi masa dadi kasancewar shekarunsa sun fara ja amma sai dai akwai masu ganin cewa tsarin zai iya kawo cikas ga Salah, wanda ya fi son kwallon zurawa da gudu.

Liberpool ba ta dauko wani sabon dan kwallo ba, wanda hakan ya sa ake tunanin har yanzu shi ne zai ja ragamar kungiyar a kakar bana amma abin jira a gani shi ne yadda za ta kaya da dan wasan a kakar bana, da kuma ganin ko kungiyar za ta sabunta kwantiraginsa a karshen kakar bana.

Yankuba Minteh

Daya daga cikin cinikin ‘yan kwallo da aka yi a kakar bana shi ne na dan wasan kwallon Gambiya, Yankuba Minteh, wanda a kakar bara ya buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Feyenoord a karkarshin mai koyarwa Arne Slo Liverpool.

Dan wasan mai shekara 20 ya koma Newcastle United ne daga kungiyar Odense ta Denmark a Yunin bara a kan kudi kusan fan miliyan biyar, amma kungiyar ta tura shi aro domin ya kara gogewa. Sai dai bayan ya jefa kwallo 10 a wasanni 27 a gasar Netherland, sai Eberton da Lyon da Borussia Dortmund suka fara zawarcinsa, amma Brighton ce ta samu nasarar dauko shi a kan £30m.

Cewa zai nuna bajinta, kamar yadda Saintfiet ya bayyana ya yi daidai, kasancewar Minteh matashin dan wasa ne mai gudu, da iya zara da iya zura kwallaye wanda hakan yasa ake ganin magoya bayan kungiyar Brighton za su yi fatan ganin ya fara kafar dama.

Thomas Partey

Lokacin da Arsenal ta kashe £ 45m ($57.8m) a kan dan wasa Thomas Partey a watan Oktoban shekara ta 2020, an sa rai sosai cewa zai kara wa tsakiyar kungiyar karfi amma duk da buga wasanni 95 a Gasar Premier a kaka hudu da ya yi, har yanzu dan wasan na Ghana bai nuna bajintar da aka yi zato ba, saboda yawan jin rauni.

A yanzu da ya rage saura shekara daya a kwantiraginsa, idan har zai iya taimakon Arsenal ta lashe Gasar Firimiyar Ingila a karon farko bayan shekara 21, hakan zai iya zama masa ban-kwana mai kyau a rayuwarsa ta kungiyar.

Pape Matar Sarr

Matashin dan wasa Matar Sarr yana daya daga cikin ‘yan wasan da suka haska a gasar cin kofin nahiyar Afirka na 2023 kuma tun a kakar bara da sabon kocin Tottenham Postecoglou ya fara aiki ne aka fara ganin alamar zai yi amfani da dan wasan na tsakiyar Senegal din.

Duk da raunin da ya samu a tsakiyar kaka a lokacin da ake hutun Afcon, dan wasan mai shekara 21 ya buga wasa 27 a Premier a kakar 2023 zuwa 2024 kuma ana kallonsa a matsayin daya daga cikin zaratan ‘yan wasan wannan zamanin a kasarsa, zai iya kara wa Tottenham din karfi?

Dan wasan na Senegal, a kakar bana dai za a zura ido a gani irin rawar da zai taka ne a kungiyar ta Tottenham kuma ana ganin yana daya daga cikin ‘yan wasan da za su taimakawa Tottenham wajen cimma burinta na kammala gasar firimiya a mataki na ‘yan hudun farko.

Kakar bara ce kaka ta biyu a tarihin Premier da kungiyoyin uku da suka shigo gasar suka yi karkon kifi, inda dukansu suka koma a Gasar Championship a shekarar kuma yanzu Ipswich Town da Leicester City da Southampton za su dage wajen ganin sun kauce wa irin abin da ya faru da kungiyoyin Burnley, Luton da Sheffield United.

Kungiyar Leicester City za ta dogara ne da ‘yan wasan Afirka da ke kungiyar, sannan sun yi farin cikin sabunta kwantiragin da fitaccen dan wasan tsakiyar Najeriya Wilfred Ndidi ya yi. Sannan dan wasan Zambia Patson Daka da dan wasan gaban Ghana Abdul Fatawu ne suka jagoranci gaban kungiyar a kakar bara, inda su ukun suka zura kwallo 12 a Gasar Championship.

Kungiyar Ipswich ta dawo Premier bayan shekara 22, inda yanzu kyaftin dinta shi ne Sam Morsy dan kasar Masar, sannan akwai Adel Tuanzebe dan kasar DR Congo a cikin ‘yan wasanta sanan ita ma Southampton tana da zaratan ‘yan wasan Afirka, inda ake sa ran dan Najeriya Joe Aribo zai nuna bajinta a kungiyar sosai a bana.

Kwanan nan ne kocin Southampton, Russell Martin ya bayyana dan wasan gaban Najeriya wanda ya yi kakar bara a kungiyar Trabzonspor a matsayin aro, a matsayin na daban bayan wasannin atisaye da suka buga.
Amma har yanzu dan wasan Ghana Kamaldeen Sulemana bai gama warware ba daga raunin wata 18 da ya yi, inda yanzu haka aka tabbatar ba zai buga wasansu na farko na sabuwar kakar ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

DSS Ta Kama Tsohon Editan BBC, Adejuwon Soyinka A Filin Jirgin Sama Na Legas

Next Post

Batun Auren “Mijin Wata” Da ‘Yan Mata Ke Yayi

Related

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
Wasanni

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

10 hours ago
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari
Wasanni

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

1 day ago
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
Wasanni

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

2 days ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Wasanni

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

3 days ago
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
Wasanni

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

3 days ago
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

5 days ago
Next Post
Ingila

Batun Auren “Mijin Wata” Da ‘Yan Mata Ke Yayi

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.