• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan APC A Kaduna Na Kokawa Kan Mayar Da Su Saniyar-ware Wajen Rabon Muƙamai

by Muhammad
2 years ago
Kaduna

Wani rahoto da BBC ta yi kan wata ɓaraka da ta kunno kai a jihar Kaduna tsakanin wasu ‘ya’yan jam’iyyar APC mai mulkin jihar dangane da rabon muƙamai a matakin gwamnatin tarayya da na Jiha.

Wasu magoya bayan jam’iyyar a yankunan karkara na zargin cewa ana nuna musu bambanci wajen rabon mukamai, duk kuwa da irin gudunmuwar da suka ce sun bayar a lokacin zaɓe.

  • Gwamnan Uba Sani Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori, Ya Nemi Su Yi Aiki Tukuru
  • PDP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Zaben Kaduna Da Ta Tabbatar Da Nasarar Uba Sani

Mutanen sun kafa hujja da wasu manyan muƙamai huɗu da suka ce an ba wa wata ƙaramar hukuma guda.

Alhaji Yusuf Owner Dutsen Wai, na ɗaya daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar APCn da ke zargin cewa ba a yi musu adalci ba wajen rabon, ya kuma shaida cewa su mutanen karkara ba a yin komai da su.

Ya ce, ‘‘Mun tura mota ne ta bar mu da hayaƙi saboda dukkan muƙaman nan da aka bayar babu wani ɗan karkara ko guda.”

LABARAI MASU NASABA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

‘‘ Tun daga kan muƙamin minista har zuwa sauran muƙamai an raba wa waɗanda ba su iya cin akwatunan zaɓensu ba, idan har gaskiya ake so idan mutum ɗan jam’iyya ne ai sai a ɗauki muƙami a ba shi ba a dunƙule abu wuri ɗaya kamar ƙwallo ba,” in ji shi.

Shi kuwa Honorabul Umar Sale Koch, daga yankin Kujama na jihar ta Kaduna, shaida wa BBC ya yi cewa, idan har jam’iyyar APCn ba ta ɗauki mataki na waiwayar yankunan karkara wajen rabon muƙaman ba, to hakan ka iya zama barazana ga jam’iyyar tasu a nan gaba.

Ya ce,“ Siyasa aba ce ta jama’a kuma har aka ci gaba da kasancewa a wannan yanayi to zai iya zama barazana ga jam’iyyarmu ta APC, domin yawan ƙuri’u da jama’ar ake samu daga karkara za su ƙaurace wa jam’iyyar.”

Dan siyasar ya ce,“ Idan aka kalli siyasar ma a yanzu gaba ɗayan waɗanda suka fito daga wata jam’iyyar suka yake mu yanzu sun dawo kuma su ne suke ta wawushe muƙaman, mu muna tsaye mun zama ‘yan kallo.”

To sai dai a nata ɓangaren jam’iyyar APC a jihar ta Kaduna ta ce kamata ya yi masu irin wannan ƙorafi su kwantar da hankalinsu kasancewar gwamnatin APCn a matakin tarayya da kuma jiha ta ƙuduri aniyar tafiya tare da kowa.

Honorabul Salisu Tanko Sono, wanda shi ne kakakin jam’iyyar APC a Kaduna, ya ce, ya kamata mutane su rinƙa haƙuri domin ita gwamnati tana da faɗi, kuma mukaman nan yanzu aka fara, mutanen da suke ganin ba a yi da su, su yi haƙuri ana sane da su.

Taƙaddama tsakanin ‘yan siyasa a Nijeriya ba sabon abu ba ne, inda a wasu lokutan har takan kai a samu rarrabuwar kai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10
Manyan Labarai

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Next Post
An Horar Da ‘Ya’Yan Masu Bukata Ta Musanman Sana’o’in Hannu A Jihar Sokoto

An Horar Da 'Ya'Yan Masu Bukata Ta Musanman Sana'o'in Hannu A Jihar Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.