ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan APC A Kaduna Na Kokawa Kan Mayar Da Su Saniyar-ware Wajen Rabon Muƙamai

by Muhammad
3 years ago
Kaduna

Wani rahoto da BBC ta yi kan wata ɓaraka da ta kunno kai a jihar Kaduna tsakanin wasu ‘ya’yan jam’iyyar APC mai mulkin jihar dangane da rabon muƙamai a matakin gwamnatin tarayya da na Jiha.

Wasu magoya bayan jam’iyyar a yankunan karkara na zargin cewa ana nuna musu bambanci wajen rabon mukamai, duk kuwa da irin gudunmuwar da suka ce sun bayar a lokacin zaɓe.

  • Gwamnan Uba Sani Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori, Ya Nemi Su Yi Aiki Tukuru
  • PDP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Zaben Kaduna Da Ta Tabbatar Da Nasarar Uba Sani

Mutanen sun kafa hujja da wasu manyan muƙamai huɗu da suka ce an ba wa wata ƙaramar hukuma guda.

ADVERTISEMENT

Alhaji Yusuf Owner Dutsen Wai, na ɗaya daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar APCn da ke zargin cewa ba a yi musu adalci ba wajen rabon, ya kuma shaida cewa su mutanen karkara ba a yin komai da su.

Ya ce, ‘‘Mun tura mota ne ta bar mu da hayaƙi saboda dukkan muƙaman nan da aka bayar babu wani ɗan karkara ko guda.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘‘ Tun daga kan muƙamin minista har zuwa sauran muƙamai an raba wa waɗanda ba su iya cin akwatunan zaɓensu ba, idan har gaskiya ake so idan mutum ɗan jam’iyya ne ai sai a ɗauki muƙami a ba shi ba a dunƙule abu wuri ɗaya kamar ƙwallo ba,” in ji shi.

Shi kuwa Honorabul Umar Sale Koch, daga yankin Kujama na jihar ta Kaduna, shaida wa BBC ya yi cewa, idan har jam’iyyar APCn ba ta ɗauki mataki na waiwayar yankunan karkara wajen rabon muƙaman ba, to hakan ka iya zama barazana ga jam’iyyar tasu a nan gaba.

Ya ce,“ Siyasa aba ce ta jama’a kuma har aka ci gaba da kasancewa a wannan yanayi to zai iya zama barazana ga jam’iyyarmu ta APC, domin yawan ƙuri’u da jama’ar ake samu daga karkara za su ƙaurace wa jam’iyyar.”

Dan siyasar ya ce,“ Idan aka kalli siyasar ma a yanzu gaba ɗayan waɗanda suka fito daga wata jam’iyyar suka yake mu yanzu sun dawo kuma su ne suke ta wawushe muƙaman, mu muna tsaye mun zama ‘yan kallo.”

To sai dai a nata ɓangaren jam’iyyar APC a jihar ta Kaduna ta ce kamata ya yi masu irin wannan ƙorafi su kwantar da hankalinsu kasancewar gwamnatin APCn a matakin tarayya da kuma jiha ta ƙuduri aniyar tafiya tare da kowa.

Honorabul Salisu Tanko Sono, wanda shi ne kakakin jam’iyyar APC a Kaduna, ya ce, ya kamata mutane su rinƙa haƙuri domin ita gwamnati tana da faɗi, kuma mukaman nan yanzu aka fara, mutanen da suke ganin ba a yi da su, su yi haƙuri ana sane da su.

Taƙaddama tsakanin ‘yan siyasa a Nijeriya ba sabon abu ba ne, inda a wasu lokutan har takan kai a samu rarrabuwar kai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyya.

Kaduna
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Next Post
An Horar Da ‘Ya’Yan Masu Bukata Ta Musanman Sana’o’in Hannu A Jihar Sokoto

An Horar Da 'Ya'Yan Masu Bukata Ta Musanman Sana'o'in Hannu A Jihar Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.