ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan APC A Kaduna Na Kokawa Kan Mayar Da Su Saniyar-ware Wajen Rabon Muƙamai

by Muhammad
3 years ago
Kaduna

Wani rahoto da BBC ta yi kan wata ɓaraka da ta kunno kai a jihar Kaduna tsakanin wasu ‘ya’yan jam’iyyar APC mai mulkin jihar dangane da rabon muƙamai a matakin gwamnatin tarayya da na Jiha.

Wasu magoya bayan jam’iyyar a yankunan karkara na zargin cewa ana nuna musu bambanci wajen rabon mukamai, duk kuwa da irin gudunmuwar da suka ce sun bayar a lokacin zaɓe.

  • Gwamnan Uba Sani Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori, Ya Nemi Su Yi Aiki Tukuru
  • PDP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Zaben Kaduna Da Ta Tabbatar Da Nasarar Uba Sani

Mutanen sun kafa hujja da wasu manyan muƙamai huɗu da suka ce an ba wa wata ƙaramar hukuma guda.

ADVERTISEMENT

Alhaji Yusuf Owner Dutsen Wai, na ɗaya daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar APCn da ke zargin cewa ba a yi musu adalci ba wajen rabon, ya kuma shaida cewa su mutanen karkara ba a yin komai da su.

Ya ce, ‘‘Mun tura mota ne ta bar mu da hayaƙi saboda dukkan muƙaman nan da aka bayar babu wani ɗan karkara ko guda.”

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

‘‘ Tun daga kan muƙamin minista har zuwa sauran muƙamai an raba wa waɗanda ba su iya cin akwatunan zaɓensu ba, idan har gaskiya ake so idan mutum ɗan jam’iyya ne ai sai a ɗauki muƙami a ba shi ba a dunƙule abu wuri ɗaya kamar ƙwallo ba,” in ji shi.

Shi kuwa Honorabul Umar Sale Koch, daga yankin Kujama na jihar ta Kaduna, shaida wa BBC ya yi cewa, idan har jam’iyyar APCn ba ta ɗauki mataki na waiwayar yankunan karkara wajen rabon muƙaman ba, to hakan ka iya zama barazana ga jam’iyyar tasu a nan gaba.

Ya ce,“ Siyasa aba ce ta jama’a kuma har aka ci gaba da kasancewa a wannan yanayi to zai iya zama barazana ga jam’iyyarmu ta APC, domin yawan ƙuri’u da jama’ar ake samu daga karkara za su ƙaurace wa jam’iyyar.”

Dan siyasar ya ce,“ Idan aka kalli siyasar ma a yanzu gaba ɗayan waɗanda suka fito daga wata jam’iyyar suka yake mu yanzu sun dawo kuma su ne suke ta wawushe muƙaman, mu muna tsaye mun zama ‘yan kallo.”

To sai dai a nata ɓangaren jam’iyyar APC a jihar ta Kaduna ta ce kamata ya yi masu irin wannan ƙorafi su kwantar da hankalinsu kasancewar gwamnatin APCn a matakin tarayya da kuma jiha ta ƙuduri aniyar tafiya tare da kowa.

Honorabul Salisu Tanko Sono, wanda shi ne kakakin jam’iyyar APC a Kaduna, ya ce, ya kamata mutane su rinƙa haƙuri domin ita gwamnati tana da faɗi, kuma mukaman nan yanzu aka fara, mutanen da suke ganin ba a yi da su, su yi haƙuri ana sane da su.

Taƙaddama tsakanin ‘yan siyasa a Nijeriya ba sabon abu ba ne, inda a wasu lokutan har takan kai a samu rarrabuwar kai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyya.

Kaduna
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
An Horar Da ‘Ya’Yan Masu Bukata Ta Musanman Sana’o’in Hannu A Jihar Sokoto

An Horar Da 'Ya'Yan Masu Bukata Ta Musanman Sana'o'in Hannu A Jihar Sokoto

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.