Ana zargin cewa an kashe tsohowar shugaban kotun gargajiya ta jihar Benue, Misis Margaret Igbeta a gidanta da ke layin Wantor Kwange a cikin garin Makurdi.
Igbeta mai shekara 72 a duniya an tsinci gawarta kwance cikin jini a daren ranar Alhamis.
- Shugabannin Sin Da Afirka Sun Yi Tattaunawa Kan Zamanintar Da Kasa
- Firimiyar Bana:Wasanni Uku Da Za Su Fi Daukar Hankalin Masu Kallo
Rahotonni sun cewa an gano gawar mamaciyar ne a ranar Juma’a da safiya bayan da makasanta da har yanzu ba a san ko su waye ba suka aiwatar da aika-aikar nasu.
‘Yansanda sun dauko gawarta daga gidanta da ke kusa da kwalejin BSU a kan layin Gboko a Makurdi.
Majiya daga bangaren ‘yansanda ta shaida wa ‘yan jarida cewa, “Eh gaskiya ne a jiya (Ranar Alhamis) an tsinci gawarta a cikin gidanta.”
Majiyar ya kara da cewa ‘yansanda suna ta kokarin yadda za a bi wajen cafko makasanta tare da gurfanar da su a gaban kuliya.
Da aka tuntubi kakakin ‘yansandan jihar, SP Catherine Anene, ta ce za ta binciki hakikanin abun da ya faru kafin bayyana wa ‘yan jarida.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp