ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliya: NEMA Ta Bada Tallafin Kayayyakin Agaji Ga Mutane 22,202 A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Kebbi

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) tare da hadin gwiwar gwamnatin Jihar Kebbi ta hanyar Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jihar (SEMA) sun ba da tallafin kayan agaji ga magidanta 22,202 da aka tabbatar a shekarar 2022 wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a fadin kananan hukumomi 21 na jihar.

An gudanar da bikin raba kayan tallafin a Bulasa a yau Juma’a a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohowar Shugaban Kotun Gargajiya A Benue
  • Firimiyar Bana:Wasanni Uku Da Za Su Fi Daukar Hankalin Masu Kallo

Amma za a gudanar da raba kayan kan fuska biyu kuma za a fara kashi na farko a yau ga mutane 9,101 da abin ya shafa.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin, Darakta Janar na NEMA Mustapha Habib, ya ce a shekarar 2022 an samu yawaitar ambaliyar ruwa a jahohin tarayya da dama kuma jihar Kebbi na daya daga ciki, bisa ga hakan ne aka hada da ma’aikatan NEMA tare da hadin gwiwar hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Kebbi SEMA aka tantance dukkanin iyalan da abin ya shafa a fadin kananan hukumomi 21 na jihar tare da tantance irin abin da suka rasa.

“Mun samu damar tantancewa tare da tantance iyalai 22,202 da abin ya shafa a ambaliyar ruwan shekarar 2022 a jihar Kebbi da gwamnatin tarayya sun amince da bayar da gudunmawar tallafin kayan agaji ga duk wadanda abin ya shafa a fadin kasar,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Darakta Janar na NEMA, wanda ya samu wakilcin Alhaji Ismail Yusuf ya ci gaba da cewa, a wannan shekarar an tantance mutane 864,854 a fadin kasar amma kuma jihar Kebbi tana da mutane 22,202 da abin ya shafa.

Don haka a yau mun zo ne domin kaddamar da bikin raba kayan agajin da aka baiwa jihar Kebbi.

“Mun bayar da gudummawar kayayyakin agaji ga jihar Kebbi kamar haka: injin mika, keken dinki, katifa, mayafi, gidan sauro, bokiti, kayan girki, shinkafa da man Gyada. Sannan kayan aikin gona su sun hada da: irin shinkafa (Paddy Rice Seeds), maganin kwari, injinan ban ruwan shukka, zuwa ga dukkan iyalan da abin ya shafa da aka tabbatar da su” in ji shi”.

Ya kuma yi kira ga wadanda suka ci gajiyar tallafin a jihar da kada su sayar da ko daya daga cikin kayayyakin da aka ba su, wani abin jin dadi ne da gwamnatin tarayya ta ce ta yi domin ta tausaya muku tare da nuna damuwa kan abin da ya same ku.

A kan wannan bayanin, na yi kira ga dukanku da ku yi amfani da wadannan abubuwan ta hanyar da ya dace.

“Muna yi muku fatan alheri kuma za mu ci gaba da ba ku tallafi don samun damar ci gaba da gudanar da harkokin ku na yau da kullum, mun gode muku baki daya, muna kuma mika godiyarmu ga gwamnan jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris da SEMA kan yadda suke ci gaba da gudanar da harkokin ku na yau da kullum. Haka Kuma ya yaba ga irin kyakkyawar alakar aiki da fahimtar juna a fannin gudanar da ayyukanmu na doka a duk lokacin da abin ya taso. Ya yaba.”

Da yake jawabi a wajen taron kaddamar da rabon kayan, Gwamna Nasir Idris wanda mataimakinsa Sanata Abubakar Umar Tafida ya wakilta, ya bada tabbacin ga gwamnatin tarayya da kuma shugaban hukumar NEMA wajen raba dukkan kayayyakin da aka bayar ga wadanda abin ya shafa a jihar Kebbi da yardar Allah ba tare da wata matsala ba, inji shi”.

Gwamnan ya ce “Tuni gwamnatin jihar ta kafa kwamitin da zai kula da rabon kayayyakin tare da tabbatar da an kai ga dukkan gidajen da aka tantance da ambaliyar ruwa ta shafa a shekarar 2022 a jihar,” in ji shi.

Ya yi wa shugaban hukumar NEMA alkawarin cewa babu wani daga cikin wadanda abin ya shafa a jihar da zai sayar da duk wani kayan da aka bayar, domin wani bangare na aikin kwamitin shi ne tabbatar da cewa babu wanda ya sayar da kayansa da kuma lura da yadda ake amfani da shi.

Ya kuma bayyana cewa, dukkan kwamishinoni a kananan hukumomin da abin ya shafa,Mai su bada shawara ga gwamna , shugabannin kananan Hukumomi da kansiloli da sauran su za su kasance shugabannin kwamitoci da mambobin da aka dora musu alhakin tabbatar da duk kayayyakin da aka bayar ga wadanda abin ya shafa za su samu kayan su ba tare da karkatar da su ba, da kuma tabbatar da cewa sun yi amfani da su ta hanyar da ya dace, bisa ga hakan ya yi gargadin cewa kayayyakin su kai ga wadanda abin ya shafa”.

Haka zalika, ya yi kira ga wadanda suka ci gajiyar tallafin da su tabbatar da yin amfani da duk kayayyakin da aka ba su ta hanyar da ya dace tare da ci gaba da marawa gwamnatin tarayya da jihar k6ebbi baya karkashin jagorancin Bola Ahmed Tunibu da Dakta Nasir Idris goyon bayan.

Bugu da kari ya ce karin tallafi da abubuwan jin dadi za su same ku nan ba da jimawa ba, don haka ku ci gaba da amince da gwamnatin domin tana da tsare-tsare masu yawa zuwa gare ku.

Daga karshe ya bayyana jin dadinsa bisa tallafin kayan agaji ga jiharsa da kuma ‘yan uwa da abin ya shafa, mun godewa gwamnatin tarayya da kuma Darakta Janar na NEMA bisa tallafin da suke bai wa jihar Kebbi.

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Zamfara Za Ta Bai Wa Mata Fifiko Wajen Walwalarsu

Gwamnatin Zamfara Za Ta Bai Wa Mata Fifiko Wajen Walwalarsu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.