ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliya: NEMA Ta Bada Tallafin Kayayyakin Agaji Ga Mutane 22,202 A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Kebbi

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) tare da hadin gwiwar gwamnatin Jihar Kebbi ta hanyar Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jihar (SEMA) sun ba da tallafin kayan agaji ga magidanta 22,202 da aka tabbatar a shekarar 2022 wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a fadin kananan hukumomi 21 na jihar.

An gudanar da bikin raba kayan tallafin a Bulasa a yau Juma’a a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohowar Shugaban Kotun Gargajiya A Benue
  • Firimiyar Bana:Wasanni Uku Da Za Su Fi Daukar Hankalin Masu Kallo

Amma za a gudanar da raba kayan kan fuska biyu kuma za a fara kashi na farko a yau ga mutane 9,101 da abin ya shafa.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin, Darakta Janar na NEMA Mustapha Habib, ya ce a shekarar 2022 an samu yawaitar ambaliyar ruwa a jahohin tarayya da dama kuma jihar Kebbi na daya daga ciki, bisa ga hakan ne aka hada da ma’aikatan NEMA tare da hadin gwiwar hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Kebbi SEMA aka tantance dukkanin iyalan da abin ya shafa a fadin kananan hukumomi 21 na jihar tare da tantance irin abin da suka rasa.

“Mun samu damar tantancewa tare da tantance iyalai 22,202 da abin ya shafa a ambaliyar ruwan shekarar 2022 a jihar Kebbi da gwamnatin tarayya sun amince da bayar da gudunmawar tallafin kayan agaji ga duk wadanda abin ya shafa a fadin kasar,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Darakta Janar na NEMA, wanda ya samu wakilcin Alhaji Ismail Yusuf ya ci gaba da cewa, a wannan shekarar an tantance mutane 864,854 a fadin kasar amma kuma jihar Kebbi tana da mutane 22,202 da abin ya shafa.

Don haka a yau mun zo ne domin kaddamar da bikin raba kayan agajin da aka baiwa jihar Kebbi.

“Mun bayar da gudummawar kayayyakin agaji ga jihar Kebbi kamar haka: injin mika, keken dinki, katifa, mayafi, gidan sauro, bokiti, kayan girki, shinkafa da man Gyada. Sannan kayan aikin gona su sun hada da: irin shinkafa (Paddy Rice Seeds), maganin kwari, injinan ban ruwan shukka, zuwa ga dukkan iyalan da abin ya shafa da aka tabbatar da su” in ji shi”.

Ya kuma yi kira ga wadanda suka ci gajiyar tallafin a jihar da kada su sayar da ko daya daga cikin kayayyakin da aka ba su, wani abin jin dadi ne da gwamnatin tarayya ta ce ta yi domin ta tausaya muku tare da nuna damuwa kan abin da ya same ku.

A kan wannan bayanin, na yi kira ga dukanku da ku yi amfani da wadannan abubuwan ta hanyar da ya dace.

“Muna yi muku fatan alheri kuma za mu ci gaba da ba ku tallafi don samun damar ci gaba da gudanar da harkokin ku na yau da kullum, mun gode muku baki daya, muna kuma mika godiyarmu ga gwamnan jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris da SEMA kan yadda suke ci gaba da gudanar da harkokin ku na yau da kullum. Haka Kuma ya yaba ga irin kyakkyawar alakar aiki da fahimtar juna a fannin gudanar da ayyukanmu na doka a duk lokacin da abin ya taso. Ya yaba.”

Da yake jawabi a wajen taron kaddamar da rabon kayan, Gwamna Nasir Idris wanda mataimakinsa Sanata Abubakar Umar Tafida ya wakilta, ya bada tabbacin ga gwamnatin tarayya da kuma shugaban hukumar NEMA wajen raba dukkan kayayyakin da aka bayar ga wadanda abin ya shafa a jihar Kebbi da yardar Allah ba tare da wata matsala ba, inji shi”.

Gwamnan ya ce “Tuni gwamnatin jihar ta kafa kwamitin da zai kula da rabon kayayyakin tare da tabbatar da an kai ga dukkan gidajen da aka tantance da ambaliyar ruwa ta shafa a shekarar 2022 a jihar,” in ji shi.

Ya yi wa shugaban hukumar NEMA alkawarin cewa babu wani daga cikin wadanda abin ya shafa a jihar da zai sayar da duk wani kayan da aka bayar, domin wani bangare na aikin kwamitin shi ne tabbatar da cewa babu wanda ya sayar da kayansa da kuma lura da yadda ake amfani da shi.

Ya kuma bayyana cewa, dukkan kwamishinoni a kananan hukumomin da abin ya shafa,Mai su bada shawara ga gwamna , shugabannin kananan Hukumomi da kansiloli da sauran su za su kasance shugabannin kwamitoci da mambobin da aka dora musu alhakin tabbatar da duk kayayyakin da aka bayar ga wadanda abin ya shafa za su samu kayan su ba tare da karkatar da su ba, da kuma tabbatar da cewa sun yi amfani da su ta hanyar da ya dace, bisa ga hakan ya yi gargadin cewa kayayyakin su kai ga wadanda abin ya shafa”.

Haka zalika, ya yi kira ga wadanda suka ci gajiyar tallafin da su tabbatar da yin amfani da duk kayayyakin da aka ba su ta hanyar da ya dace tare da ci gaba da marawa gwamnatin tarayya da jihar k6ebbi baya karkashin jagorancin Bola Ahmed Tunibu da Dakta Nasir Idris goyon bayan.

Bugu da kari ya ce karin tallafi da abubuwan jin dadi za su same ku nan ba da jimawa ba, don haka ku ci gaba da amince da gwamnatin domin tana da tsare-tsare masu yawa zuwa gare ku.

Daga karshe ya bayyana jin dadinsa bisa tallafin kayan agaji ga jiharsa da kuma ‘yan uwa da abin ya shafa, mun godewa gwamnatin tarayya da kuma Darakta Janar na NEMA bisa tallafin da suke bai wa jihar Kebbi.

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Zamfara Za Ta Bai Wa Mata Fifiko Wajen Walwalarsu

Gwamnatin Zamfara Za Ta Bai Wa Mata Fifiko Wajen Walwalarsu

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.