ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliya: NEMA Ta Bada Tallafin Kayayyakin Agaji Ga Mutane 22,202 A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Kebbi

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) tare da hadin gwiwar gwamnatin Jihar Kebbi ta hanyar Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jihar (SEMA) sun ba da tallafin kayan agaji ga magidanta 22,202 da aka tabbatar a shekarar 2022 wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a fadin kananan hukumomi 21 na jihar.

An gudanar da bikin raba kayan tallafin a Bulasa a yau Juma’a a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohowar Shugaban Kotun Gargajiya A Benue
  • Firimiyar Bana:Wasanni Uku Da Za Su Fi Daukar Hankalin Masu Kallo

Amma za a gudanar da raba kayan kan fuska biyu kuma za a fara kashi na farko a yau ga mutane 9,101 da abin ya shafa.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin, Darakta Janar na NEMA Mustapha Habib, ya ce a shekarar 2022 an samu yawaitar ambaliyar ruwa a jahohin tarayya da dama kuma jihar Kebbi na daya daga ciki, bisa ga hakan ne aka hada da ma’aikatan NEMA tare da hadin gwiwar hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Kebbi SEMA aka tantance dukkanin iyalan da abin ya shafa a fadin kananan hukumomi 21 na jihar tare da tantance irin abin da suka rasa.

“Mun samu damar tantancewa tare da tantance iyalai 22,202 da abin ya shafa a ambaliyar ruwan shekarar 2022 a jihar Kebbi da gwamnatin tarayya sun amince da bayar da gudunmawar tallafin kayan agaji ga duk wadanda abin ya shafa a fadin kasar,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Darakta Janar na NEMA, wanda ya samu wakilcin Alhaji Ismail Yusuf ya ci gaba da cewa, a wannan shekarar an tantance mutane 864,854 a fadin kasar amma kuma jihar Kebbi tana da mutane 22,202 da abin ya shafa.

Don haka a yau mun zo ne domin kaddamar da bikin raba kayan agajin da aka baiwa jihar Kebbi.

“Mun bayar da gudummawar kayayyakin agaji ga jihar Kebbi kamar haka: injin mika, keken dinki, katifa, mayafi, gidan sauro, bokiti, kayan girki, shinkafa da man Gyada. Sannan kayan aikin gona su sun hada da: irin shinkafa (Paddy Rice Seeds), maganin kwari, injinan ban ruwan shukka, zuwa ga dukkan iyalan da abin ya shafa da aka tabbatar da su” in ji shi”.

Ya kuma yi kira ga wadanda suka ci gajiyar tallafin a jihar da kada su sayar da ko daya daga cikin kayayyakin da aka ba su, wani abin jin dadi ne da gwamnatin tarayya ta ce ta yi domin ta tausaya muku tare da nuna damuwa kan abin da ya same ku.

A kan wannan bayanin, na yi kira ga dukanku da ku yi amfani da wadannan abubuwan ta hanyar da ya dace.

“Muna yi muku fatan alheri kuma za mu ci gaba da ba ku tallafi don samun damar ci gaba da gudanar da harkokin ku na yau da kullum, mun gode muku baki daya, muna kuma mika godiyarmu ga gwamnan jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris da SEMA kan yadda suke ci gaba da gudanar da harkokin ku na yau da kullum. Haka Kuma ya yaba ga irin kyakkyawar alakar aiki da fahimtar juna a fannin gudanar da ayyukanmu na doka a duk lokacin da abin ya taso. Ya yaba.”

Da yake jawabi a wajen taron kaddamar da rabon kayan, Gwamna Nasir Idris wanda mataimakinsa Sanata Abubakar Umar Tafida ya wakilta, ya bada tabbacin ga gwamnatin tarayya da kuma shugaban hukumar NEMA wajen raba dukkan kayayyakin da aka bayar ga wadanda abin ya shafa a jihar Kebbi da yardar Allah ba tare da wata matsala ba, inji shi”.

Gwamnan ya ce “Tuni gwamnatin jihar ta kafa kwamitin da zai kula da rabon kayayyakin tare da tabbatar da an kai ga dukkan gidajen da aka tantance da ambaliyar ruwa ta shafa a shekarar 2022 a jihar,” in ji shi.

Ya yi wa shugaban hukumar NEMA alkawarin cewa babu wani daga cikin wadanda abin ya shafa a jihar da zai sayar da duk wani kayan da aka bayar, domin wani bangare na aikin kwamitin shi ne tabbatar da cewa babu wanda ya sayar da kayansa da kuma lura da yadda ake amfani da shi.

Ya kuma bayyana cewa, dukkan kwamishinoni a kananan hukumomin da abin ya shafa,Mai su bada shawara ga gwamna , shugabannin kananan Hukumomi da kansiloli da sauran su za su kasance shugabannin kwamitoci da mambobin da aka dora musu alhakin tabbatar da duk kayayyakin da aka bayar ga wadanda abin ya shafa za su samu kayan su ba tare da karkatar da su ba, da kuma tabbatar da cewa sun yi amfani da su ta hanyar da ya dace, bisa ga hakan ya yi gargadin cewa kayayyakin su kai ga wadanda abin ya shafa”.

Haka zalika, ya yi kira ga wadanda suka ci gajiyar tallafin da su tabbatar da yin amfani da duk kayayyakin da aka ba su ta hanyar da ya dace tare da ci gaba da marawa gwamnatin tarayya da jihar k6ebbi baya karkashin jagorancin Bola Ahmed Tunibu da Dakta Nasir Idris goyon bayan.

Bugu da kari ya ce karin tallafi da abubuwan jin dadi za su same ku nan ba da jimawa ba, don haka ku ci gaba da amince da gwamnatin domin tana da tsare-tsare masu yawa zuwa gare ku.

Daga karshe ya bayyana jin dadinsa bisa tallafin kayan agaji ga jiharsa da kuma ‘yan uwa da abin ya shafa, mun godewa gwamnatin tarayya da kuma Darakta Janar na NEMA bisa tallafin da suke bai wa jihar Kebbi.

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Gwamnatin Zamfara Za Ta Bai Wa Mata Fifiko Wajen Walwalarsu

Gwamnatin Zamfara Za Ta Bai Wa Mata Fifiko Wajen Walwalarsu

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.