• English
  • Business News
Monday, June 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Shingen Bincike Na ‘Yan Sanda Sun Harbe Mutum 2 A Ebonyi

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Fada Ya Barke Tsakanin Shugabannin ’Yan Bindiga, 2 Sun Mutu Yayin Rikicin A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kashe mutane biyu, dan sanda daya da daya daga cikin wadanda ake zargin na daga cikin ‘yan bindigar da suka kai hari a shingen binciken jami’an ‘yan sanda da ke kan titin G-Hostel Junction na babbar hanyar Enugu zuwa Abakaliki a jihar Ebonyi, a ranar Laraba da yamma, bayan wani hari da suka kai wa ‘yan sanda.

Lamarin dai kamar yadda LEADERSHIP ta rawaito, an ce ya faru ne a mahadar da ke kusa da babbar mahadar Presco a Abakaliki, babban birnin jihar.

  • Matawalle Ya Amince Da Hukuncin Kisa Kan Masu Garkuwa Da Masu Ba ‘Yan Bindiga Bayanan Sirri
  • Harin Jirgin Kasa: Saura Fasinjoji 27 A Hannun ‘Yan Bindiga

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ebonyi, SP Chris Anyanwu, ya ce ko da yake lamarin ya faru, amma ya kara da cewa har yanzu ba a kai ga tantance lamarin ba har zuwa lokacin da ake hada wannan labarin.

Ya ce rundunar ta sanar da jami’in ‘yan sanda na yankin (DPO) na yankin domin samun cikakken bayani game da harin, inda ya kara da cewa har yanzu bai samu cikakken bayanin harin ba.

“Na je wani shiri na dawo ofis yanzu, ana ta yada jita-jitar harin a shafukan sada zumunta amma ba zan iya ba da cikakken bayani ba a yanzu, na kira DPO na yankin kuma ina jiransa. don ba mu cikakken bayani.

Labarai Masu Nasaba

Matawalle: Kofarmu Abude Take Idan Gwamna Dauda Lawal Na San Shigowa Jamiyyar APC

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

“Mutane na cewa an harbe dan sanda daya har lahira amma ba zan iya tabbatar da hakan ba a halin yanzu, akwai kuma wani rade-radin cewa an kama daya daga cikin ‘yan bindigar amma har yanzu ana ta yada jita-jita, cikakken bayani zai zo idan muka samu cikakken rahoto daga DPO,” in ji PPRO.

LEADERSHIP ta tattaro cewa ‘yan bindigar wadanda adadinsu ya kai uku sun yi amfani da baburan hawa.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun bude wuta kan ‘yan sandan da ke shingen binciken, inda nan take suka kashe daya daga cikinsu.

A fafatawar da aka yi da bindigar, an ce ‘yan sandan sun harbe daya daga cikin maharan a daidai lokacin da sauran biyun suka tsere a kan babur.

Lamarin dai ya haifar da firgici da tashin hankali a babbar mahadar inda ‘yan kasuwa da masu shaguna da masu ababen hawa da masu wucewa suka yi ta tururuwa domin tsira da rayukansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Cafke Mutumin Da Zai Aike Da Bindigu Kano Daga Abuja Ta Tashar Mota

Next Post

Buhari Ya Bude Rukunin Gidajen Da Gwamna Zulum Ya Gina Wa Malamai A Jihar Borno

Related

Matawalle: Kofarmu Abude Take Idan Gwamna Dauda Lawal Na San Shigowa Jamiyyar APC
Labarai

Matawalle: Kofarmu Abude Take Idan Gwamna Dauda Lawal Na San Shigowa Jamiyyar APC

10 minutes ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

2 hours ago
Mutum 3 Sun Rasu, 15 Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota A Hanyar Kano
Labarai

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa

4 hours ago
Gwamnatin Gombe Ta Yi Albishir Ɗin Gina Babban Zangon Noma Da Kiwo Ɗauke Da Kasuwar Duniya A Jihar 
Manyan Labarai

Gwamnatin Gombe Ta Yi Albishir Ɗin Gina Babban Zangon Noma Da Kiwo Ɗauke Da Kasuwar Duniya A Jihar 

5 hours ago
Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”
Manyan Labarai

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

17 hours ago
Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

18 hours ago
Next Post
Buhari Ya Bude Rukunin Gidajen Da Gwamna Zulum Ya Gina Wa Malamai A Jihar Borno

Buhari Ya Bude Rukunin Gidajen Da Gwamna Zulum Ya Gina Wa Malamai A Jihar Borno

LABARAI MASU NASABA

Matawalle: Kofarmu Abude Take Idan Gwamna Dauda Lawal Na San Shigowa Jamiyyar APC

Matawalle: Kofarmu Abude Take Idan Gwamna Dauda Lawal Na San Shigowa Jamiyyar APC

June 9, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 11 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

June 9, 2025
Mutum 3 Sun Rasu, 15 Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota A Hanyar Kano

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 9 A Jigawa

June 9, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Yi Albishir Ɗin Gina Babban Zangon Noma Da Kiwo Ɗauke Da Kasuwar Duniya A Jihar 

Gwamnatin Gombe Ta Yi Albishir Ɗin Gina Babban Zangon Noma Da Kiwo Ɗauke Da Kasuwar Duniya A Jihar 

June 9, 2025
He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

June 8, 2025
Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

June 8, 2025
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

June 8, 2025
Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

June 8, 2025
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.