Rundunar ‘yansandan jihar Benuwe ta tabbatar da garkuwa da dukkan fasinjojin wata motar bas ta kamfanin Benue Links a hanyar Eke, Ugbokolo a karamar hukumar Okpokwu ta jihar a yammacin Lahadi.
Wani ganau da ya zanta da LEADERSHIP ta wayar tarho, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 7 na yammacin ranar Lahadi, inda wasu ‘yan bindigar suka tare wata motar bas din da ta taho daga Abeokuta, babban birnin jihar Ogun, suka yi awon gaba da fasinjojin da ke cikinta bayan sun kwace kayayyakinsu, sannan suka tafi da su cikin daji.
- 2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega
- Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Benuwe, Edet Udeme ya bayyana cewa, lamarin ya rutsa ne da wata motar bas kirar Toyota mai lamba 14B-143BN, wadda aka same ta a gefen titi a Ugbokolo, cikin karamar hukumar Okokwu.
A cewar Udeme, da samun rahoton lamarin, tawagar ‘yansanda tare da hadin gwiwar sojoji da kuma ‘yan sa kai na al’ummar jihar Benuwe, suka yi gaggawar zuwa wurin.
“A lokacin da rundunar ta tsunduma dajin, ta ceto daya daga cikin fasinjojin, mai suna Paul Terns, wanda ya yi nasarar tserewa daga hannun masu garkuwar”.
Udeme ta kara da cewa, an tura karin wasu sojoji a yankin domin kara kaimi wajen neman sauran fasinjojin da kuma tabbatar da dawowarsu cikin koshin lafiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp