Al’ummar Udei da ke karamar hukumar Guma a jihar Benuwe sun shiga fargaba biyo bayan kashe jami’an ‘yansanda hudu a yayin da suke dakile wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai wa al’ummar yankin a ranar Lahadi.
Wakilinmu ya tattaro cewa, ‘yan bindigar da suka yi yunkurin kai hari a lokaci guda kan al’ummar Daudu, Tse Asongu, da Tse Asha amma sun fuskanci turjiya, sai dai sun kashe jami’an ‘yansanda hudu a Tse da ke Udei.
Wata majiya a yankin da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa wakilinmu ta wayar tarho cewa, ‘yan bindigar sun yi yunkurin kutsawa sansanin ‘yan gudun hijira na Ortese, amma rundunar hadin gwiwar jami’an tsaro da ke yankin suka dakile harin.
Wani matashi a yankin wanda ya bayyana sunansa da Kaase, ya ce ‘yan bindigar a yunkurinsu na farko sun yi kokarin afkawa garin Daudu amma jami’an tsaro suka dakile su, sai suka tafi Tse Asongu da Asha amma al’ummar garuruwan duk sun gudu kafin isowar su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp