Akalla mutane takwas ne suka mutu a wani sabon harin da wasu ‘yan bindiga suka kai a kauyen Chicim da ke karamar hukumar Mangu ta jihar Filato.
Wata majiya mai tushe ta ce mutane takwas ne suka mutu yayin da wasu uku da suka samu raunuka ke karbar magani a wani Asibiti da ba a bayyana sunansa ba.
- Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu
- Shugabannin Sin Da Kongo (Brazaville) Sun Aike Da Wasikun Taya Murna Ga Taron Ministocin Kula Da Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC
Mazauna yankin da suka zanta da wakilinmu ta wayar tarho sun ce ‘yan bindigar sun far wa al’ummar yankin da ke da nisan kilomita daya daga garin Mangu da misalin karfe 10 na daren ranar Talata inda suka fara harbe kan duk wani abu da ya gittaya kan hanyarsu.
Wani ganau mai suna Kespan Iliya wanda shi ma mazaunin unguwar ne ya shaida wa manema labarai cewa, ‘yan unguwar na cikin barci lokacin da ‘yan bindigar suka iso cikin shigar kwamandoji, inda suka rika harbe-harbe kan mazauna unguwar.
LEADERSHIP ta fahimci cewa, sama da gidaje 96 ne kuma aka kone a Gyenbwas, al’ummar gundumar Langai ta karamar hukumar Mangu a yayin harin.
Kokarin jin ta bakin jami’im yada labarai na rundunar ‘Operation Save Haven (OPSH)’, Manjo Samson Zhakom ya ci tura domin wayarsa a kashe take a lokacin rubuta wannan rahoto.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp