• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Yi Mana Tayin Miliyan 10 Mu Saki ‘Yan Uwansu Amma Mun Ki Karba – NSCDC

by Abubakar Abba
3 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Yi Mana Tayin Miliyan 10 Mu Saki ‘Yan Uwansu Amma Mun Ki Karba – NSCDC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar tsaro ta farin kaya ta (NSCDC) a jihar Sokoto, a karshen mako ta baje kolin wasu gaggan masu garkuwa da mutane biyu da suka addabi yankunan Silame, Binji, Gudu, Tureta da karamar hukumar Dange/Shuni a jihar.

Bayan nasarar cafke su, tawagar masu garkuwan sun nemi jami’an tsaron da suke sake ‘yan uwansu, za su ba Jami’an cin hanci na naira miliyan 10.

  • Yadda ‘Yan Bindiga Suka Hallaka Ma’aikata Hudu Da ‘Yansanda Biyu A Kamfanin Sarrafa Tasa

Da yake magana da ‘yan jarida a Sokoto, Kwamandan hukumar a jihar, Muhammad Dada, ya ce wadanda suka cafke sun hada da Alhaji Koire da Alhaji Buba, sun kasance ‘yan bindiga masu hatsarin gaske da suke da sama da mabiya 300 da suke addabar mutane.

Muhammad ya ce ‘yan ta’addan, “Sun addabi al’ummar Silame, Binji, Gudu, Tureta da karamar hukumar Dange/Shuni da ke jihar.

“Lokacin da na samu labarin inda suke boya a maboyarsu da ke karamar hukumar Silame. Ni da kaina na jagoranci tawagata zuwa can inda muka shafe kwanaki biyu a cikin daji, mun kuma sami nasarar kamo su bisa wannan farmakin da muka kai.

Labarai Masu Nasaba

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

“Bayan da muka kama su ‘yan tawagarsu sun yi kokarin ba mu cin hanci na miliyan 10 domin mu sake wadanda muka kama.”

Daga nan ya sha alwashin cewa za su kara azama da kwazo tare da takwarorinsu na tsaro domin tabbatar da dakile aniyar bata-garin da suka addabi al’umma.

Alhaji Buba, da bakinsa ya ce ya shiga harkar garkuwa da mutanen karamar hukumar Dabegi Dange/ Shuni inda suka amshi kudin fansa na naira miliyan 4 da kuma yin wani garkuwan a Kudula a karamar hukumar Gudu inda suka karbi miliyan 1 na fansa.

Ya ce suna da shugaba a Jamhuriyar Nijar mai suna Danbuzu da yake musu safaran bindiga AK-47 da alburusai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa 17 A Filato

Next Post

An Yi Artabu Tsakanin ‘Yansanda Da Zaunagari-banza A Abuja

Related

Bindiga
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

2 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

2 hours ago
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma
Labarai

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

3 hours ago
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

3 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 19-09-2025

4 hours ago
Bindiga
Labarai

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

5 hours ago
Next Post
An Yi Artabu Tsakanin ‘Yansanda Da Zaunagari-banza A Abuja

An Yi Artabu Tsakanin ‘Yansanda Da Zaunagari-banza A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Bindiga

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Bindiga

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.