• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Hallaka Ma’aikata Hudu Da ‘Yansanda Biyu A Kamfanin Sarrafa Tasa

by Ahmed Muhammed Danasabe
3 years ago
in Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 36 A Wani Sabon Hari A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan bindiga da ba a san kosu wane ne ba sun kai mummunar hari a kamfanin sarrafa tasa da ke Ajaokuta a Jihar Kogi, inda suka hallaka mutum shida da suka hada da ma’aikata ‘yan kasashen waje biyu da direbobin kamfanin biyu da kuma jami’an ‘yansanda biyu tare da garkuwa da ma’aikata uku ‘yan kasashen waje da ke aiki a kamfanin. 

Harin ya zo ne bayan makonni biyu da wasu ‘yan bindiga suka kai hari kauyen Jida Bassa da ke yankin karamar hukumar ta Ajaokuta, inda suka hallaka ‘yan sanda uku da ‘yan sintiri (bijilante) biyar da kuma sace yara uku a rukunin gidaje na Kaduna da ke kamfanin sarrafa karafa na Ajaokuta, inda suka nemi a biya su kudin fansa har naira miliyan dari kafin su saki kananan yaran uku wadda shekarunsu suka kama daga biyar, bakwai zuwa goma.

  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne
  • Dariye Zai Tsaya Takarar Sanata A Filato Bayan Yi Masa Afuwa Daga Gidan Yari

Wata majiya ta shaida wa Jaridar LEADERSHIP Hausa cewa ‘yan bindigan sun shigo kamfanin sarrafa tasan da ke karamar hukumar Ajaokuta na Jihar Kogi ne da misalin karfe bakwai na daren ranar Juma’ar da ta gabata, inda suka kashe ma’aikatan kamfanin hudu da ke cikin motar bas da ke shirin kai su wurare dabam-dabam.

Wani ganau wanda ya nemi a sakaye sunansa ya ce ‘yan bindigan wadanda suka kawo harin cikin motoci biyu, sun yi wa ma’aikata ‘yan kasashen wajen da sauran ma’aikatan dak e cikin motar kamfanin kwantar bauna, inda suka fara harbin kan mai-uwada-wabi.

Ya ce, “Yau wata ranan bakin ciki ne garemu a nan Ajaokuta, muna cikin jimamin kashe jami’an tsaro bakwai da ‘yan bindiga suka yi a Jida Bassa kwanan nan da yin garkuwa da yara uku duk a nan Ajaokuta, sai gashi kuma wannan ya auku, to yaya za mu yi da rayukannu?

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

“Wadanda suka rasa rayukansu da wadanda ‘yan bindigan suka yi garkuwa da su suna shirin barin kamfanin ne zuwa masaukinsu da ke rukunun gidaje na Neja da ke Ajaokutan kafin ‘yan bindigan su yi musu kwantar bauna.

Ya ce, “Suna aiki ne a kamfanin sarrafa tasa na yammacin Afirka da ke nan Ajaokuta.

“Jami’an ‘yan sanda sun rika musayar wuta da bata-garin, amma abin takaici biyu daga cikin ‘yan sandan da direbobin kamfanin guda biyu da kuma ma’aikata ‘yan kasashen waje, sun rasa rayukansu a cikin motar kamfanin, a yayin da kuma ‘yan bindigan suka yi garkuwa da ma’aikata ‘yan kasashen waje uku,” in ji shi.

A bangare guda kuma, kwamishinan watsa labarai na Jihar Kogi, Mista Kingsley Fanwo, a martanin da yayi game da harin ya ce gwamnatin jihar ta yi Allah wadai da wannan harin.

Ya kuma kara da cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ceto wadanda aka yi garkuwa da su da kuma zakulo wadanda suka aikata wannan mummunar aiki.

Kwamishinan ya kuma ce wannan hari da sauran ayyukan bata-gari ko kadan ba zai karya wa gwambatin Jihar Kogi karkashin shugabancin Gwamna Yahaya Bello wajen kare lafiya da kuma dujiyoyin al’umma, sannan ya gargadi masu aikata laifufuka da su gaggauta sauya wani wurin don aikata laifi.

Haka shi ma kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Kogi, CP Edward Egbuka, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Kogi, Mista William Aya a wata sanarwa da ya fitar, ya ce rundunar ta fara bincike game da faruwar lamarin kuma a shirye take ta zakulo wadanda suka aikata danyen aikin.

Kawo hada wannan labarin, ‘yan bindigan ba su tuntubi iyalai ko kamfanin sarrafa tasan ba domin amsar kudin fansa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FarmakiGarkuwaHarbiHariKamfaniMa'aikataTasaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista

Next Post

Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

2 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

4 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

5 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

6 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

11 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

13 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.