• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Tuba A Kasar Nijar

by Sulaiman
11 months ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Tuba A Kasar Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ci gaba da nasara da ake yi kan mayakan Boko Haram a kasashen Nijeriya, Chadi, Kamaru, da Nijar, an sake samun wasu daga cikin ‘yan bindigar da su ka mika wuya a yankin Diffa na Jamhuriyar Nijar.

 

‘Yan Boko Haram na ci gaba da tuba a Jihar Diffa da ke gabashin Jamhuriyar Nijar da ma sauran wuraren na gabashi, inda a yanzu haka mahukunta ke cigaba da karbar tubabbun mayakan Boko Haram din wadanda suka mika wuya bisa radin kansu, a wani mataki na sake saka su a cikin al’umma amma bayan horas da su ta hanyar sauya musu tunani zuwa mai kyau.

  • Babban Kwamandan Boko Haram Da Wasu Mutane 9 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Borno
  • NIREC Ta Buƙaci Tinubu Ya Kawo Ƙarshen Rashin Tsaro A Nijeriya

Yanzu an sake samun ‘yan Boko Haram sama da 700 da su ka tuba. Wadannan tubabbun dai a halin yanzu na gudanar mu’amalar zamantakewarsu tsakaninsu da al’umma, inda sannu a hankali su ke sabawa da rayuwar yau da kullum baya ga horas da su din da za a yin a musamman.

 

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

Jihar ta Diffa, wacce ke makotaka da Nijeriya, Chadi, ta yi fama da hare-haren Boko Haram a shekarun da su ka gabata, al’amarin da ya yi sanadin mace- macen mutane da dama ciki har da yara kanana da mata.

 

Wannan ya sa da dama daga cikin ‘yan yankin sun gudu zuwa wasu sassan kasar, baya ga wadanda su ka ketara zuwa wasu kasashe makobta.

 

Idan za a iya tunawa dai, a jihar ta Diffa tun a shekara ta 2015 aka fara rikicin Boko Haram, lokacin da har ta kai ga hukumomin yankin na ta kokarin yin yarjejeniyoyin sulhu da ‘yan Boko Haram. Bayan da aka fara cimma jituwa, sai ‘yan bindigar Boko Haram din suka fara mika wuya a 2016, inda nan take aka shiga tura su a wata cibiyar da ke sake daidaita hankalinsu jihar ta Diffa.

 

A shekara ta 2019 kuwa mahukuntan Jihar Diffa na lokacin suka umurci fara tura tubabbun zuwa ga ‘yan uwansu.

 

Malam Kyari Ari, daya daga cikin tubabbun farko da suka aje makamansu a Jihar Diffa, kuma kawo yanzu suke zaman lafiya da jama’a, ya bayyana cewa an yaudare su ne suka shiga Bako Haram. Ya yi kira ga hukumomi da su taimaka musu da abin yin sana’a don samun abin zaman gari.

Su ma mutanen gari sun bayar da kyakkyawar shaida kan tubabban ‘yan Boko Haram din da cewa suna cikakken zaman lafiya da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko Haram Da ISWAPNahiyar TuraiTabarbarewar tsaro a Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Olmo Ya Jefa Kwallo A Raga A Wasan Shi Na Farko A Barcelona

Next Post

Haɗarin Kwale-kwale Ya Sake Ajalin Mutane 5 A Jigawa

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

3 hours ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

9 hours ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

13 hours ago
Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

17 hours ago
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

1 day ago
Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja
Manyan Labarai

Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

1 day ago
Next Post
Haɗarin Kwale-kwale Ya Sake Ajalin Mutane 5 A Jigawa

Haɗarin Kwale-kwale Ya Sake Ajalin Mutane 5 A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.