ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Tuba A Kasar Nijar

by Sulaiman
2 years ago
Boko Haram

A ci gaba da nasara da ake yi kan mayakan Boko Haram a kasashen Nijeriya, Chadi, Kamaru, da Nijar, an sake samun wasu daga cikin ‘yan bindigar da su ka mika wuya a yankin Diffa na Jamhuriyar Nijar.

 

‘Yan Boko Haram na ci gaba da tuba a Jihar Diffa da ke gabashin Jamhuriyar Nijar da ma sauran wuraren na gabashi, inda a yanzu haka mahukunta ke cigaba da karbar tubabbun mayakan Boko Haram din wadanda suka mika wuya bisa radin kansu, a wani mataki na sake saka su a cikin al’umma amma bayan horas da su ta hanyar sauya musu tunani zuwa mai kyau.

ADVERTISEMENT
  • Babban Kwamandan Boko Haram Da Wasu Mutane 9 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Borno
  • NIREC Ta Buƙaci Tinubu Ya Kawo Ƙarshen Rashin Tsaro A Nijeriya

Yanzu an sake samun ‘yan Boko Haram sama da 700 da su ka tuba. Wadannan tubabbun dai a halin yanzu na gudanar mu’amalar zamantakewarsu tsakaninsu da al’umma, inda sannu a hankali su ke sabawa da rayuwar yau da kullum baya ga horas da su din da za a yin a musamman.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Jihar ta Diffa, wacce ke makotaka da Nijeriya, Chadi, ta yi fama da hare-haren Boko Haram a shekarun da su ka gabata, al’amarin da ya yi sanadin mace- macen mutane da dama ciki har da yara kanana da mata.

 

Wannan ya sa da dama daga cikin ‘yan yankin sun gudu zuwa wasu sassan kasar, baya ga wadanda su ka ketara zuwa wasu kasashe makobta.

 

Idan za a iya tunawa dai, a jihar ta Diffa tun a shekara ta 2015 aka fara rikicin Boko Haram, lokacin da har ta kai ga hukumomin yankin na ta kokarin yin yarjejeniyoyin sulhu da ‘yan Boko Haram. Bayan da aka fara cimma jituwa, sai ‘yan bindigar Boko Haram din suka fara mika wuya a 2016, inda nan take aka shiga tura su a wata cibiyar da ke sake daidaita hankalinsu jihar ta Diffa.

 

A shekara ta 2019 kuwa mahukuntan Jihar Diffa na lokacin suka umurci fara tura tubabbun zuwa ga ‘yan uwansu.

 

Malam Kyari Ari, daya daga cikin tubabbun farko da suka aje makamansu a Jihar Diffa, kuma kawo yanzu suke zaman lafiya da jama’a, ya bayyana cewa an yaudare su ne suka shiga Bako Haram. Ya yi kira ga hukumomi da su taimaka musu da abin yin sana’a don samun abin zaman gari.

Su ma mutanen gari sun bayar da kyakkyawar shaida kan tubabban ‘yan Boko Haram din da cewa suna cikakken zaman lafiya da su.

Boko Haram
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Haɗarin Kwale-kwale Ya Sake Ajalin Mutane 5 A Jigawa

Haɗarin Kwale-kwale Ya Sake Ajalin Mutane 5 A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.