• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Fashi Sun Shiga Gidan Dan Wasa Donnarumma A Paris

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
‘Yan Fashi Sun Shiga Gidan Dan Wasa Donnarumma A Paris
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kai wa mai tsaron ragar kasar Italiya da Paris St-Germain, Gianluigi Donnarumma da abokiyar zamansa hari tare da yi masa fashi a gidansu da ke birnin Paris kamar yadda rahotanni suka tabbatar.

Wasu gungun mutane ne suka kai harin inda suka daure su a gidansu da ke gunduma ta takwas a tsakiyar babban birnin kasar, kamar yadda majiyar ‘yansanda ta shaida wa kafar yada labaran Faransa.

  • Tarihin Shigar Nijeriya Gasar Kofin Duniya Ta Mata

Daga nan ne dan wasan da abokiyar zamansa suka tsere zuwa wani otal da ke kusa bayan maharan sun tafi kuma ma’aikatan otal ne suka sanar wa ‘yansanda kafin aka kai su asibiti.

Kakakin ofishin mai shigar da kara na birnin Paris ya shaida wa manema labarai cewa, an fara bincike kan zargin yin fashi da makami da wata kungiya da ta shirya ta kuma gudanar cikin dare a gidan Mista Donnarumma.

Rahotannin da ba a tabbatar da su ba a shafin yada labarai na Actu17 sun ce maharan sun yi awon gaba da kayan ado da agogo da kuma kayan alatu da kudinsu ya kai Yuro 500,000 (£430,000).

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

Dan wasan ya samu rauni kadan yayin da abokiyar zamansa, Alessia Elefante, ba ta samu rauni ba, kamar yadda majiyoyi suka shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Farans.

Ofishin mai shigar da kara ya ce rundunar ‘yan sandan kasar Faransa ta musamman ta BRB da ke da alhakin yaki da fashi da makami, ya fara gudanar da bincike domin gano wadanda suka shiga gidan dan wasan.
Gianluigi Donnarumma, mai shekaru 24, ya koma Paris ne shekaru biyu da suka wuce, kuma a ranar Juma’a ne ake sa ran zai hade da tawagar Paris St-Germain gabanin wasan sada zumunta na farko da kungiyar za ta buga da Le Habre da kuma rangadin kasashen Japan da Koriya ta Kudu.

Amma Donnarumma ba shi ne dan wasan kwallon kafa na PSG na farko da ‘yan daba ke kai wa hari ba, amma galibin hare-haren da aka kai a baya an yi su ne yayin da wanda aka kai ma harin ba su gida.

A watan Janairun da ya gabata, an yanke wa wasu maza biyu hukuncin dauri a gidan yari sakamakon wani hari da su ka kai a watan Maris din shekara ta 2021 a gidan dan wasan kwallon kafar Brazil Markuinhos da ke Ybelines a yammacin birnin Paris.

Markuinhos yana wasa a lokacin da lamarin ya faru amma mahaifinsa yana gidan tare da ‘ya’yansa mata guda biyu sai dai barayin sun bugi mahaifin a fuska da kuma hakarkarinsa amma bai ji rauni ba.

Kuma har ila yau a wannan ranar ce aka yi wa gidan abokin wasan Markuinhos Angel Di Maria fashi wanda shima ba ya gida kuma aka tafi da kayayyaki daban-daban kamar yadda rahotanni suka bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

LEADERSHIP Ta Dage Taronta Kan Illar Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi

Next Post

Za A Kara Kashi 10 A Kasafin Bangaren Lafiya

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

1 day ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

1 day ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

2 days ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

3 days ago
Shekaru 15, Wasanni 578, Daga Karshe Harry Kane Ya Lashe Kofi
Wasanni

Shekaru 15, Wasanni 578, Daga Karshe Harry Kane Ya Lashe Kofi

5 days ago
Mun Fara Shirin Lashe Firimiya Ta Gaba –Slot
Wasanni

Mun Fara Shirin Lashe Firimiya Ta Gaba –Slot

5 days ago
Next Post
Za A Kara Kashi 10 A Kasafin Bangaren Lafiya

Za A Kara Kashi 10 A Kasafin Bangaren Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.