• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Fashi Sun Shiga Gidan Dan Wasa Donnarumma A Paris

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
‘Yan Fashi Sun Shiga Gidan Dan Wasa Donnarumma A Paris
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kai wa mai tsaron ragar kasar Italiya da Paris St-Germain, Gianluigi Donnarumma da abokiyar zamansa hari tare da yi masa fashi a gidansu da ke birnin Paris kamar yadda rahotanni suka tabbatar.

Wasu gungun mutane ne suka kai harin inda suka daure su a gidansu da ke gunduma ta takwas a tsakiyar babban birnin kasar, kamar yadda majiyar ‘yansanda ta shaida wa kafar yada labaran Faransa.

  • Tarihin Shigar Nijeriya Gasar Kofin Duniya Ta Mata

Daga nan ne dan wasan da abokiyar zamansa suka tsere zuwa wani otal da ke kusa bayan maharan sun tafi kuma ma’aikatan otal ne suka sanar wa ‘yansanda kafin aka kai su asibiti.

Kakakin ofishin mai shigar da kara na birnin Paris ya shaida wa manema labarai cewa, an fara bincike kan zargin yin fashi da makami da wata kungiya da ta shirya ta kuma gudanar cikin dare a gidan Mista Donnarumma.

Rahotannin da ba a tabbatar da su ba a shafin yada labarai na Actu17 sun ce maharan sun yi awon gaba da kayan ado da agogo da kuma kayan alatu da kudinsu ya kai Yuro 500,000 (£430,000).

Labarai Masu Nasaba

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan wasan ya samu rauni kadan yayin da abokiyar zamansa, Alessia Elefante, ba ta samu rauni ba, kamar yadda majiyoyi suka shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Farans.

Ofishin mai shigar da kara ya ce rundunar ‘yan sandan kasar Faransa ta musamman ta BRB da ke da alhakin yaki da fashi da makami, ya fara gudanar da bincike domin gano wadanda suka shiga gidan dan wasan.
Gianluigi Donnarumma, mai shekaru 24, ya koma Paris ne shekaru biyu da suka wuce, kuma a ranar Juma’a ne ake sa ran zai hade da tawagar Paris St-Germain gabanin wasan sada zumunta na farko da kungiyar za ta buga da Le Habre da kuma rangadin kasashen Japan da Koriya ta Kudu.

Amma Donnarumma ba shi ne dan wasan kwallon kafa na PSG na farko da ‘yan daba ke kai wa hari ba, amma galibin hare-haren da aka kai a baya an yi su ne yayin da wanda aka kai ma harin ba su gida.

A watan Janairun da ya gabata, an yanke wa wasu maza biyu hukuncin dauri a gidan yari sakamakon wani hari da su ka kai a watan Maris din shekara ta 2021 a gidan dan wasan kwallon kafar Brazil Markuinhos da ke Ybelines a yammacin birnin Paris.

Markuinhos yana wasa a lokacin da lamarin ya faru amma mahaifinsa yana gidan tare da ‘ya’yansa mata guda biyu sai dai barayin sun bugi mahaifin a fuska da kuma hakarkarinsa amma bai ji rauni ba.

Kuma har ila yau a wannan ranar ce aka yi wa gidan abokin wasan Markuinhos Angel Di Maria fashi wanda shima ba ya gida kuma aka tafi da kayayyaki daban-daban kamar yadda rahotanni suka bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

LEADERSHIP Ta Dage Taronta Kan Illar Sha Da Fataucin Miyagun Kwayoyi

Next Post

Za A Kara Kashi 10 A Kasafin Bangaren Lafiya

Related

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya
Wasanni

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

14 minutes ago
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC
Wasanni

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

30 minutes ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

2 days ago
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique
Wasanni

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

4 days ago
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense
Wasanni

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

4 days ago
Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars
Wasanni

Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars

5 days ago
Next Post
Za A Kara Kashi 10 A Kasafin Bangaren Lafiya

Za A Kara Kashi 10 A Kasafin Bangaren Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.