ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Fashi Sun Shiga Gidan Dan Wasa Donnarumma A Paris

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Donnarumma

An kai wa mai tsaron ragar kasar Italiya da Paris St-Germain, Gianluigi Donnarumma da abokiyar zamansa hari tare da yi masa fashi a gidansu da ke birnin Paris kamar yadda rahotanni suka tabbatar.

Wasu gungun mutane ne suka kai harin inda suka daure su a gidansu da ke gunduma ta takwas a tsakiyar babban birnin kasar, kamar yadda majiyar ‘yansanda ta shaida wa kafar yada labaran Faransa.

  • Tarihin Shigar Nijeriya Gasar Kofin Duniya Ta Mata

Daga nan ne dan wasan da abokiyar zamansa suka tsere zuwa wani otal da ke kusa bayan maharan sun tafi kuma ma’aikatan otal ne suka sanar wa ‘yansanda kafin aka kai su asibiti.

ADVERTISEMENT

Kakakin ofishin mai shigar da kara na birnin Paris ya shaida wa manema labarai cewa, an fara bincike kan zargin yin fashi da makami da wata kungiya da ta shirya ta kuma gudanar cikin dare a gidan Mista Donnarumma.

Rahotannin da ba a tabbatar da su ba a shafin yada labarai na Actu17 sun ce maharan sun yi awon gaba da kayan ado da agogo da kuma kayan alatu da kudinsu ya kai Yuro 500,000 (£430,000).

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Dan wasan ya samu rauni kadan yayin da abokiyar zamansa, Alessia Elefante, ba ta samu rauni ba, kamar yadda majiyoyi suka shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Farans.

Ofishin mai shigar da kara ya ce rundunar ‘yan sandan kasar Faransa ta musamman ta BRB da ke da alhakin yaki da fashi da makami, ya fara gudanar da bincike domin gano wadanda suka shiga gidan dan wasan.
Gianluigi Donnarumma, mai shekaru 24, ya koma Paris ne shekaru biyu da suka wuce, kuma a ranar Juma’a ne ake sa ran zai hade da tawagar Paris St-Germain gabanin wasan sada zumunta na farko da kungiyar za ta buga da Le Habre da kuma rangadin kasashen Japan da Koriya ta Kudu.

Amma Donnarumma ba shi ne dan wasan kwallon kafa na PSG na farko da ‘yan daba ke kai wa hari ba, amma galibin hare-haren da aka kai a baya an yi su ne yayin da wanda aka kai ma harin ba su gida.

A watan Janairun da ya gabata, an yanke wa wasu maza biyu hukuncin dauri a gidan yari sakamakon wani hari da su ka kai a watan Maris din shekara ta 2021 a gidan dan wasan kwallon kafar Brazil Markuinhos da ke Ybelines a yammacin birnin Paris.

Markuinhos yana wasa a lokacin da lamarin ya faru amma mahaifinsa yana gidan tare da ‘ya’yansa mata guda biyu sai dai barayin sun bugi mahaifin a fuska da kuma hakarkarinsa amma bai ji rauni ba.

Kuma har ila yau a wannan ranar ce aka yi wa gidan abokin wasan Markuinhos Angel Di Maria fashi wanda shima ba ya gida kuma aka tafi da kayayyaki daban-daban kamar yadda rahotanni suka bayyana.

Donnarumma
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Za A Kara Kashi 10 A Kasafin Bangaren Lafiya

Za A Kara Kashi 10 A Kasafin Bangaren Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.