• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Fashin Daji Sun Sace Shanu Sama Da 200 Da Raguna A Wata Gona A Jihar Sakkwato

by Muhammad
3 years ago
'Yan

A jiya ne wasu mahara da ake zaton ‘yan fashin daji ne suka kai wani hari gonakin Sarki Gobir Adiya inda suka yi awon gaba da shanu sama da 200 da raguna da dama.

Babbar gonar wacce ta shafe sama da shekaru 40 tana da ma’aikata kusan 80 mallakin Alhaji Abdullahi S. Adiya, tana da ‘yan mitoci zuwa filin jirgin saman Sultan Abubakar III da tazarar kilomita 10 daga babban birnin jihar.

  • Yadda ‘Yan Bindiga Suka Buɗe Wa Mahajjatan Sakkwato Wuta
  • ‘Yan Bindigar Da Suka Kai Wa Maniyyata Hari A Sakkwato Sun Kashe ‘Yan Sanda 6

Da yake bayyana wa wakilinmu harin, Alhaji Adiya ya ce dabbobin da aka sace su ne wadanda ake sa ran za a sayar da su domin bukukuwan Sallah mai zuwa.

A cewarsa, “Na bar gonar zuwa gidana, bayan tsakar dare kuma babu wani tunanin cewa za a kai wa gonar hari.

“A safiyar yau ne aka ta da ni, tare da labarin cewa an kai wa gonar hari, an kuma sace wasu garken shanu, raguna da tumaki da ake sa ran za mu sayar a wannan bikin na Sallah mai zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

“Lokacin da aka garzaya zuwa gonar, bayanin da jami’an tsaro suka yi kawai shi ne, suna cikin shiri har karfe 3 na safe, sai kawai suka gano cewa an sace shanun da safiyar yau.

“Sun dawo da raguna goma sha takwas, da shanu goma sha bakwai, da bijimai biyu suna yawo a cikin daji. Asarar ba ta da iyaka. Muna magana ne game da satar dabbobi a cikin kewayon sama da ɗari biyu.”

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto, ASP Abubakar Sanusi, ya ce babu wani rahoton da aka kai wa ‘yan sanda kan adadin dabbobin da aka sace.

ASP Sanusi ya ce, “Lokacin da muka samu labarin harin, nan take muka tura mutanenmu gona. Sai dai ana ci gaba da gudanar da bincike kuma za a sanar da ku yadda ya kamata.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Next Post
An Kashe Mutum 4 A Wani Rikici Tsakanin Hausawa Da Kabilar Lunguda A Adamawa

2023: Fintiri Zai Dauki Hannatu Kadala A Mataimakiyarsa, Binani Zata Sauya Namdas Da Titsi

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.