• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Fashin Daji Sun Sace Shanu Sama Da 200 Da Raguna A Wata Gona A Jihar Sakkwato

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
‘Yan Fashin Daji Sun Sace Shanu Sama Da 200 Da Raguna A Wata Gona A Jihar Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya ne wasu mahara da ake zaton ‘yan fashin daji ne suka kai wani hari gonakin Sarki Gobir Adiya inda suka yi awon gaba da shanu sama da 200 da raguna da dama.

Babbar gonar wacce ta shafe sama da shekaru 40 tana da ma’aikata kusan 80 mallakin Alhaji Abdullahi S. Adiya, tana da ‘yan mitoci zuwa filin jirgin saman Sultan Abubakar III da tazarar kilomita 10 daga babban birnin jihar.

  • Yadda ‘Yan Bindiga Suka Buɗe Wa Mahajjatan Sakkwato Wuta
  • ‘Yan Bindigar Da Suka Kai Wa Maniyyata Hari A Sakkwato Sun Kashe ‘Yan Sanda 6

Da yake bayyana wa wakilinmu harin, Alhaji Adiya ya ce dabbobin da aka sace su ne wadanda ake sa ran za a sayar da su domin bukukuwan Sallah mai zuwa.

A cewarsa, “Na bar gonar zuwa gidana, bayan tsakar dare kuma babu wani tunanin cewa za a kai wa gonar hari.

“A safiyar yau ne aka ta da ni, tare da labarin cewa an kai wa gonar hari, an kuma sace wasu garken shanu, raguna da tumaki da ake sa ran za mu sayar a wannan bikin na Sallah mai zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

“Lokacin da aka garzaya zuwa gonar, bayanin da jami’an tsaro suka yi kawai shi ne, suna cikin shiri har karfe 3 na safe, sai kawai suka gano cewa an sace shanun da safiyar yau.

“Sun dawo da raguna goma sha takwas, da shanu goma sha bakwai, da bijimai biyu suna yawo a cikin daji. Asarar ba ta da iyaka. Muna magana ne game da satar dabbobi a cikin kewayon sama da ɗari biyu.”

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto, ASP Abubakar Sanusi, ya ce babu wani rahoton da aka kai wa ‘yan sanda kan adadin dabbobin da aka sace.

ASP Sanusi ya ce, “Lokacin da muka samu labarin harin, nan take muka tura mutanenmu gona. Sai dai ana ci gaba da gudanar da bincike kuma za a sanar da ku yadda ya kamata.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Satar ShanuShanu
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Tashi Garuruwa 30 A Zamfara Da Bayar Da Umarnin Tashin Wasu 5 A Jihar Filato

Next Post

2023: Fintiri Zai Dauki Hannatu Kadala A Mataimakiyarsa, Binani Zata Sauya Namdas Da Titsi

Related

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

6 hours ago
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
Labarai

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

7 hours ago
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
Labarai

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

7 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

9 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

11 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

11 hours ago
Next Post
An Kashe Mutum 4 A Wani Rikici Tsakanin Hausawa Da Kabilar Lunguda A Adamawa

2023: Fintiri Zai Dauki Hannatu Kadala A Mataimakiyarsa, Binani Zata Sauya Namdas Da Titsi

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.