• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Fashin Daji Sun Sace Shanu Sama Da 200 Da Raguna A Wata Gona A Jihar Sakkwato

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
‘Yan Fashin Daji Sun Sace Shanu Sama Da 200 Da Raguna A Wata Gona A Jihar Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya ne wasu mahara da ake zaton ‘yan fashin daji ne suka kai wani hari gonakin Sarki Gobir Adiya inda suka yi awon gaba da shanu sama da 200 da raguna da dama.

Babbar gonar wacce ta shafe sama da shekaru 40 tana da ma’aikata kusan 80 mallakin Alhaji Abdullahi S. Adiya, tana da ‘yan mitoci zuwa filin jirgin saman Sultan Abubakar III da tazarar kilomita 10 daga babban birnin jihar.

  • Yadda ‘Yan Bindiga Suka Buɗe Wa Mahajjatan Sakkwato Wuta
  • ‘Yan Bindigar Da Suka Kai Wa Maniyyata Hari A Sakkwato Sun Kashe ‘Yan Sanda 6

Da yake bayyana wa wakilinmu harin, Alhaji Adiya ya ce dabbobin da aka sace su ne wadanda ake sa ran za a sayar da su domin bukukuwan Sallah mai zuwa.

A cewarsa, “Na bar gonar zuwa gidana, bayan tsakar dare kuma babu wani tunanin cewa za a kai wa gonar hari.

“A safiyar yau ne aka ta da ni, tare da labarin cewa an kai wa gonar hari, an kuma sace wasu garken shanu, raguna da tumaki da ake sa ran za mu sayar a wannan bikin na Sallah mai zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

“Lokacin da aka garzaya zuwa gonar, bayanin da jami’an tsaro suka yi kawai shi ne, suna cikin shiri har karfe 3 na safe, sai kawai suka gano cewa an sace shanun da safiyar yau.

“Sun dawo da raguna goma sha takwas, da shanu goma sha bakwai, da bijimai biyu suna yawo a cikin daji. Asarar ba ta da iyaka. Muna magana ne game da satar dabbobi a cikin kewayon sama da ɗari biyu.”

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto, ASP Abubakar Sanusi, ya ce babu wani rahoton da aka kai wa ‘yan sanda kan adadin dabbobin da aka sace.

ASP Sanusi ya ce, “Lokacin da muka samu labarin harin, nan take muka tura mutanenmu gona. Sai dai ana ci gaba da gudanar da bincike kuma za a sanar da ku yadda ya kamata.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Satar ShanuShanu
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Tashi Garuruwa 30 A Zamfara Da Bayar Da Umarnin Tashin Wasu 5 A Jihar Filato

Next Post

2023: Fintiri Zai Dauki Hannatu Kadala A Mataimakiyarsa, Binani Zata Sauya Namdas Da Titsi

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

60 minutes ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

2 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

2 hours ago
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu
Labarai

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

4 hours ago
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya
Labarai

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

6 hours ago
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 
Labarai

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

7 hours ago
Next Post
An Kashe Mutum 4 A Wani Rikici Tsakanin Hausawa Da Kabilar Lunguda A Adamawa

2023: Fintiri Zai Dauki Hannatu Kadala A Mataimakiyarsa, Binani Zata Sauya Namdas Da Titsi

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

Hanyoyin Kare Kai Daga Cutar Basir Cikin Sauƙi

September 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

September 7, 2025
Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

September 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

September 7, 2025
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.