‘Yan fashin daji sama da 100 ne suka tsere daga maboyarsu da ke dazukan yankunan Iche, Taka-Lafiya Gidan Makeri da Janjala a karamar hukumar Kagarko a Jihar Kaduna.Â
Sun tsere ne, bayan sojoji sun kutsa cikin dazukan da ke a karamar hukumar Kagarko.
- Wasu Matasa Sun Kone Ofishin Jakadancin Sweden A Iraki Kan Kona Alkur’ani Mai Tsarki
- An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa
An ruwaito cewa yankuna da dama ne ‘yan bindiga suka mamaye a Kagarko, inda suke yin garkuwa da mutane a ‘yan watanni da suka gabata.
Sai dai an samu saukin sace-sacen mutane, biyo bayan sojiji sun tarwatsa mafakar tasu a dajin, tare da kuma cafke wasu da ake zargin masu kai wa ‘yan bindiga bayanan sirri ne.
An ruwaito wani mai rike da sarautar gargajiya a Kagarko Suleiman Aliyu, ya bayyana cewa sojojin sun shiga garin Kagarko a jiya Laraba da misalin karfe 11 na safe.
Aliyu, ya ce “sun shigo garin ne a cikin motocin su kirar Hilux da wasu manyan motoci wasu kuma akan babura, inda suka wuce kai tsaye zuwa cikin kauyen Iche, Taka-Lafiya, Gidan Makeri da Janjala har zuwa cikin dajin domin farautar ‘yan bindiga a dajin.
A cewarsa, bayan da ‘yan bindigar suka samu bayanan sirri sai suka tsere daga maboyar tasu.
Wata majiya a fadar sarkin Kagarko wadda ba ta bukaci a sakaya sunanta ba ta tabbatar da shigar sojojin cikin dajin.
Kakakin rundunar ‘yansandan jihar bai fitar da wata sanarwar kan lamarin ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp