ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Matasa Sun Kone Ofishin Jakadancin Sweden A Iraki Kan Kona Alkur’ani Mai Tsarki

by Sadiq
3 years ago
Sweden

Daruruwan masu zanga-zanga ne suka mamaye ofishin jakadancin Sweden da ke Bagadaza, babban birnin kasar Iraki saboda kone wani Alkur’ani mai tsarki da aka yi a Stockholm, babban birnin kasar Sweden.

Masu zanga-zangar sun zagaye katangar ginin da sanyin safiyar ranar Alhamis tare da cinna mata wuta.

  • An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa
  • Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara

Zanga-zangar ta zo ne makonni bayan Salwan Momika, dan kasar Iraki mai shekaru 37 da haihuwa, wanda ya tsere zuwa kasar Sweden shekaru da dama, ya kone wasu shafukan littafin Alkur’ani mai tsarki, a daidai lokacin da musulmi suke gudanar da bukukuwan Idin babbar sallah a watan Yuni.

ADVERTISEMENT

Matakin na Momika ya jawo kakkausar suka daga kasashe da dama, inda Muqtada Sadr, wani malamin Shi’a mai fada a ji a Iraki, ya yi kira da a gudanar da zanga-zangar adawa da Sweden tare da korar jakadan Sweden.

An gudanar da zanga-zanga guda biyu a wajen ofishin jakadancin Sweden da ke Bagadaza bayan kone Alkur’ani, inda masu zanga-zangar suka keta harabar ofishin jakadancin.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

A ranar Laraba, ‘yansandan Sweden sun ba da takardar neman “taron jama’a” ga mutane biyu a wajen ofishin jakadancin Iraki a Stockholm a ranar Alhamis.

Ko da yake ‘yansanda ba su bayyana abin da masu zanga-zangar ke shirin yi ba, kafafen yada labaran Sweden sun ruwaito cewa mutanen biyu ciki har da Momika sun shirya kone Alkur’ani da tutar Iraki a wurin taron jama’ar.

Da take mayar da martani akan sabuwar zanga-zangar, ma’aikatar harkokin wajen Sweden ta ce dukkan ma’aikatan ofishin jakadancin Bagadaza suna cikin koshin lafiya, tare da yin Allah wadai da harin.

Har ila yau ma’aikatar harkokin wajen Iraki ta nuna rashin jin dadi kan harin da aka kai ofishin jakadancin kasar Sweden, inda ta yi alkawarin gurfanar da wadanda suka kai harin a gaban kuliya.

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
‘Yan Fashin Daji Sun Tsere Yayin Da Sojoji Suka Yi Wa Dajin Kaduna Kawanya

'Yan Fashin Daji Sun Tsere Yayin Da Sojoji Suka Yi Wa Dajin Kaduna Kawanya

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.