ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Matasa Sun Kone Ofishin Jakadancin Sweden A Iraki Kan Kona Alkur’ani Mai Tsarki

by Sadiq
3 years ago
Sweden

Daruruwan masu zanga-zanga ne suka mamaye ofishin jakadancin Sweden da ke Bagadaza, babban birnin kasar Iraki saboda kone wani Alkur’ani mai tsarki da aka yi a Stockholm, babban birnin kasar Sweden.

Masu zanga-zangar sun zagaye katangar ginin da sanyin safiyar ranar Alhamis tare da cinna mata wuta.

  • An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa
  • Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara

Zanga-zangar ta zo ne makonni bayan Salwan Momika, dan kasar Iraki mai shekaru 37 da haihuwa, wanda ya tsere zuwa kasar Sweden shekaru da dama, ya kone wasu shafukan littafin Alkur’ani mai tsarki, a daidai lokacin da musulmi suke gudanar da bukukuwan Idin babbar sallah a watan Yuni.

ADVERTISEMENT

Matakin na Momika ya jawo kakkausar suka daga kasashe da dama, inda Muqtada Sadr, wani malamin Shi’a mai fada a ji a Iraki, ya yi kira da a gudanar da zanga-zangar adawa da Sweden tare da korar jakadan Sweden.

An gudanar da zanga-zanga guda biyu a wajen ofishin jakadancin Sweden da ke Bagadaza bayan kone Alkur’ani, inda masu zanga-zangar suka keta harabar ofishin jakadancin.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

A ranar Laraba, ‘yansandan Sweden sun ba da takardar neman “taron jama’a” ga mutane biyu a wajen ofishin jakadancin Iraki a Stockholm a ranar Alhamis.

Ko da yake ‘yansanda ba su bayyana abin da masu zanga-zangar ke shirin yi ba, kafafen yada labaran Sweden sun ruwaito cewa mutanen biyu ciki har da Momika sun shirya kone Alkur’ani da tutar Iraki a wurin taron jama’ar.

Da take mayar da martani akan sabuwar zanga-zangar, ma’aikatar harkokin wajen Sweden ta ce dukkan ma’aikatan ofishin jakadancin Bagadaza suna cikin koshin lafiya, tare da yin Allah wadai da harin.

Har ila yau ma’aikatar harkokin wajen Iraki ta nuna rashin jin dadi kan harin da aka kai ofishin jakadancin kasar Sweden, inda ta yi alkawarin gurfanar da wadanda suka kai harin a gaban kuliya.

MASU ALAKA

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta
Manyan Labarai

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

July 3, 2026
Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki

July 3, 2026
Next Post
‘Yan Fashin Daji Sun Tsere Yayin Da Sojoji Suka Yi Wa Dajin Kaduna Kawanya

'Yan Fashin Daji Sun Tsere Yayin Da Sojoji Suka Yi Wa Dajin Kaduna Kawanya

LABARAI MASU NASABA

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.