ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Matasa Sun Kone Ofishin Jakadancin Sweden A Iraki Kan Kona Alkur’ani Mai Tsarki

by Sadiq
3 years ago
Sweden

Daruruwan masu zanga-zanga ne suka mamaye ofishin jakadancin Sweden da ke Bagadaza, babban birnin kasar Iraki saboda kone wani Alkur’ani mai tsarki da aka yi a Stockholm, babban birnin kasar Sweden.

Masu zanga-zangar sun zagaye katangar ginin da sanyin safiyar ranar Alhamis tare da cinna mata wuta.

  • An Rufe Makarantu A Kenya Saboda Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa
  • Babu Sulhu Tsakaninmu Da ‘Yan Fashin Daji -Gwamnatin Zamfara

Zanga-zangar ta zo ne makonni bayan Salwan Momika, dan kasar Iraki mai shekaru 37 da haihuwa, wanda ya tsere zuwa kasar Sweden shekaru da dama, ya kone wasu shafukan littafin Alkur’ani mai tsarki, a daidai lokacin da musulmi suke gudanar da bukukuwan Idin babbar sallah a watan Yuni.

ADVERTISEMENT

Matakin na Momika ya jawo kakkausar suka daga kasashe da dama, inda Muqtada Sadr, wani malamin Shi’a mai fada a ji a Iraki, ya yi kira da a gudanar da zanga-zangar adawa da Sweden tare da korar jakadan Sweden.

An gudanar da zanga-zanga guda biyu a wajen ofishin jakadancin Sweden da ke Bagadaza bayan kone Alkur’ani, inda masu zanga-zangar suka keta harabar ofishin jakadancin.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

A ranar Laraba, ‘yansandan Sweden sun ba da takardar neman “taron jama’a” ga mutane biyu a wajen ofishin jakadancin Iraki a Stockholm a ranar Alhamis.

Ko da yake ‘yansanda ba su bayyana abin da masu zanga-zangar ke shirin yi ba, kafafen yada labaran Sweden sun ruwaito cewa mutanen biyu ciki har da Momika sun shirya kone Alkur’ani da tutar Iraki a wurin taron jama’ar.

Da take mayar da martani akan sabuwar zanga-zangar, ma’aikatar harkokin wajen Sweden ta ce dukkan ma’aikatan ofishin jakadancin Bagadaza suna cikin koshin lafiya, tare da yin Allah wadai da harin.

Har ila yau ma’aikatar harkokin wajen Iraki ta nuna rashin jin dadi kan harin da aka kai ofishin jakadancin kasar Sweden, inda ta yi alkawarin gurfanar da wadanda suka kai harin a gaban kuliya.

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
‘Yan Fashin Daji Sun Tsere Yayin Da Sojoji Suka Yi Wa Dajin Kaduna Kawanya

'Yan Fashin Daji Sun Tsere Yayin Da Sojoji Suka Yi Wa Dajin Kaduna Kawanya

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.