• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar wakilai ta tarayya, ta tuhumi ma’aikatu da hukumomin gwamnati da badakalar kudade sama da Naira biliyan 103.8, wadanda suka yi daidai da dalar Amurka 950,912.05.  

Hakan na faruwa ne, yayin da majalisar ta bukaci hukumar EFCC da ICPC da sauran hukumomin da ke da alaka da su, da su bi ma’aikatu da hukumomin gwamnati, domin kwato kudaden tare da tura su asusun baitul-mali.

  • Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi
  • Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Wannan ya biyo bayan kudirin da dan majalisa mai wakiltar Bamidele Salam ya gabatar a ranar Talata, bisa sakamakon binciken da kwamitin kula da asusun gwamnati (PAC) ya yi, a yayin nazarin rahoton shekara-shekara na mai babban binciken kudi na shekarun da suka kare a ranar 31 ga Disambar 2019 da kuma 31 ga watan Disambar 2020, ciki har da binciken da ya shafi gazawar cikin gida da kuma gazawar gwamnati.

Dangane da matakin tsayiwar daka na majalisar, shawarwarin da aka amince na nufin tabbatar da bin doka ta hanyar bayar da umarnin kwato kudaden jama’a da kuma sanya takunkumi a wurin da ya zama wajibi a sanya.

Daga cikin cibiyoyin da aka ayyana wajen yin binciken a 2019, akwai ma’aikatar harkokin wajen kasar, inda aka same tad a laifin kashe kudade ba tare da izini ba, kan aikin masaukin shugaban kasa a ofishin jakadancin Nijeriya da ke Habasha.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

Kwamitin ya nemi a mayar da sama da Naira miliyan 124, kusan dala 795,000 zuwa asusun gwamnatin tarayya, an kuma bayar da karin wasu kudade da suka hada da Naira miliyan 31.7 da dala 155,923.00, a matsayin wadanda aka kashe ba bisa ka’ida ba.

An umarci ma’aikatar da ta kwato Naira miliyan 49.4 da aka biya, domin yin gyaran ba tare da bin ka’idojin sayen kayayyakin ba. Kazalika, an raba Naira miliyan 9.2 ga jami’an ofishin jakadancin, ba tare da cikakkiyar shaida ba.

Haka nan kuma, an binciki bankin noma; kan basussuka kimanin Naira biliyan 75.6.

Kwamitin ya umarci hukumar da ta buga jerin sunayen wadanda ake bi bashi a akalla a jaridu guda uku na wannan kasa tare da yin kira ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawar da su kwato wadannan makudan kudade.

Haka nan, dole ne a kwato karin Naira miliyan 350; kana kuma a gabatar da shedu cikin kwanaki 90.

Sannan, an umarci hukumar kula da gidajen yari ta Nijeriya da ta dawo tare da tura Naira miliyan 7.47 na harajin da ba ta biya ba.

Haka zalika, an umarci hukumar kula da fitar da kayayyaki ta Nijeriya (NEPZA), da ta kwaso motoci takwas na hukumar tare da tabbatar da dawo da guda hudu da ma’aikatar masana’antu, kasuwanci da zuba jari ta rike ba bisa ka’ida ba.

An kuma bayyana (NEPZA) da laifin karkatar da sama da Naira miliyan 12 tare da sanya takunkumi ga jami’in da kula da harkokin kudi.

An gurfanar da Karamar Hukumar Kwali da ke babban birnin tarayya gaban kuliya, bisa zargin biyan kudi kimanin Naira miliyan 82 da aka raba wasu mutane su 105 da ba a san ko su wane ne ba.

Kazalika, an bukaci tsohon shugaban majalisa day a dawo da kudade zuwa asusun gwamnatin tarayya tare da wasu shaidun day a mika wa kwamitin.

Haka nan, an umarci hukumar kwastam ta Nijeriya da ta yi aiki tare da Akanta Janar na Tarayya, domin samar da cikakken jerin dukkannin abubuwan da aka bai wa asusun tarayya da wadanda ban a tarayya, don tabbatar da hakikanin kudaden da ake da su.

A hukumar samar da wutar lantarki ta karkara kuma, an bankado badakalar kudi sama da Naira biliyan 1.3.

Haka nan, an umarci tsohon manajan darakta da ya mayar da Naira miliyan 394 da ya batar kan ayyukan wutar lantarki da hukumar tattalin arziki ta kasa ta amince da shi.

Bugu da kari, akwai kuma kudaden da suka hada da Naira miliyan 4.2 da aka kashe wajen aiwatar da tallace-tallace, ba a kan ka’ida bad a kuma canza Naira miliyan 969 zuwa Yuro, shi ma ba a kan ka’ida ba, tare kuma da ba da shawarar daukar matakan ladabtarwa ga jami’an da ked a alhakin gudanar da ayyukansu.

An samu kungiya kula da dabbobi ta Nijeriya da badakalar kudaden haraji na duti da kuma sauran kudaden haraji da suke karba.

An bai wa kungiyar umarnin dawo da Naira miliyan 1.1 na harajin dutin daga hannun ‘yan kwangila tare da kuma dawo da sama da Naira miliyan 19 na wasu kudade.

Yayin da majalisa ke karbar rahoton kwamitin, ta yi kira ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawa daban-daban da suka hada da EFCC, ICPC da FIRS da su kwato wadannan kudade.

Kwamitin ya kuma kara jaddada bukatar gaggauta bai wa shugabannin hukumomi damar nada masu binciken kudi daga waje, inda kuma ya bayar da shawarwarin yin gyara ga ka’idojin kudi ko wata takardar da sakataren gwamnatin tarayya zai bayar.

Mataimakin kakakin kajalisar, Rt. Hon. Benjamin Kalu, wanda ya jagoranci zaman majalisar tare da sauran ‘yan majalisa, sun yaba wad an majalisa Salam da sauran ‘yan kwamitin, bisa ga kwazon da suka nuna wajen samar da wannan cikakken rahoto.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fahimtar Sabon Tunani: Mene Ne Birnin Zamani Na Al’umma

Next Post

An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

Related

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

2 hours ago
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

4 hours ago
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama
Manyan Labarai

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

6 hours ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

6 hours ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

8 hours ago
Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja
Labarai

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

11 hours ago
Next Post
An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

September 9, 2025
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

September 9, 2025
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.