• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

by CGTN Hausa and Sulaiman
17 hours ago
in Labarai
0
majalisar kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar wakilai ta tarayya, ta tuhumi ma’aikatu da hukumomin gwamnati da badakalar kudade sama da Naira biliyan 103.8, wadanda suka yi daidai da dalar Amurka 950,912.05.  

Hakan na faruwa ne, yayin da majalisar ta bukaci hukumar EFCC da ICPC da sauran hukumomin da ke da alaka da su, da su bi ma’aikatu da hukumomin gwamnati, domin kwato kudaden tare da tura su asusun baitul-mali.

  • Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi
  • Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Wannan ya biyo bayan kudirin da dan majalisa mai wakiltar Bamidele Salam ya gabatar a ranar Talata, bisa sakamakon binciken da kwamitin kula da asusun gwamnati (PAC) ya yi, a yayin nazarin rahoton shekara-shekara na mai babban binciken kudi na shekarun da suka kare a ranar 31 ga Disambar 2019 da kuma 31 ga watan Disambar 2020, ciki har da binciken da ya shafi gazawar cikin gida da kuma gazawar gwamnati.

Dangane da matakin tsayiwar daka na majalisar, shawarwarin da aka amince na nufin tabbatar da bin doka ta hanyar bayar da umarnin kwato kudaden jama’a da kuma sanya takunkumi a wurin da ya zama wajibi a sanya.

Daga cikin cibiyoyin da aka ayyana wajen yin binciken a 2019, akwai ma’aikatar harkokin wajen kasar, inda aka same tad a laifin kashe kudade ba tare da izini ba, kan aikin masaukin shugaban kasa a ofishin jakadancin Nijeriya da ke Habasha.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

Kwamitin ya nemi a mayar da sama da Naira miliyan 124, kusan dala 795,000 zuwa asusun gwamnatin tarayya, an kuma bayar da karin wasu kudade da suka hada da Naira miliyan 31.7 da dala 155,923.00, a matsayin wadanda aka kashe ba bisa ka’ida ba.

An umarci ma’aikatar da ta kwato Naira miliyan 49.4 da aka biya, domin yin gyaran ba tare da bin ka’idojin sayen kayayyakin ba. Kazalika, an raba Naira miliyan 9.2 ga jami’an ofishin jakadancin, ba tare da cikakkiyar shaida ba.

Haka nan kuma, an binciki bankin noma; kan basussuka kimanin Naira biliyan 75.6.

Kwamitin ya umarci hukumar da ta buga jerin sunayen wadanda ake bi bashi a akalla a jaridu guda uku na wannan kasa tare da yin kira ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawar da su kwato wadannan makudan kudade.

Haka nan, dole ne a kwato karin Naira miliyan 350; kana kuma a gabatar da shedu cikin kwanaki 90.

Sannan, an umarci hukumar kula da gidajen yari ta Nijeriya da ta dawo tare da tura Naira miliyan 7.47 na harajin da ba ta biya ba.

Haka zalika, an umarci hukumar kula da fitar da kayayyaki ta Nijeriya (NEPZA), da ta kwaso motoci takwas na hukumar tare da tabbatar da dawo da guda hudu da ma’aikatar masana’antu, kasuwanci da zuba jari ta rike ba bisa ka’ida ba.

An kuma bayyana (NEPZA) da laifin karkatar da sama da Naira miliyan 12 tare da sanya takunkumi ga jami’in da kula da harkokin kudi.

An gurfanar da Karamar Hukumar Kwali da ke babban birnin tarayya gaban kuliya, bisa zargin biyan kudi kimanin Naira miliyan 82 da aka raba wasu mutane su 105 da ba a san ko su wane ne ba.

Kazalika, an bukaci tsohon shugaban majalisa day a dawo da kudade zuwa asusun gwamnatin tarayya tare da wasu shaidun day a mika wa kwamitin.

Haka nan, an umarci hukumar kwastam ta Nijeriya da ta yi aiki tare da Akanta Janar na Tarayya, domin samar da cikakken jerin dukkannin abubuwan da aka bai wa asusun tarayya da wadanda ban a tarayya, don tabbatar da hakikanin kudaden da ake da su.

A hukumar samar da wutar lantarki ta karkara kuma, an bankado badakalar kudi sama da Naira biliyan 1.3.

Haka nan, an umarci tsohon manajan darakta da ya mayar da Naira miliyan 394 da ya batar kan ayyukan wutar lantarki da hukumar tattalin arziki ta kasa ta amince da shi.

Bugu da kari, akwai kuma kudaden da suka hada da Naira miliyan 4.2 da aka kashe wajen aiwatar da tallace-tallace, ba a kan ka’ida bad a kuma canza Naira miliyan 969 zuwa Yuro, shi ma ba a kan ka’ida ba, tare kuma da ba da shawarar daukar matakan ladabtarwa ga jami’an da ked a alhakin gudanar da ayyukansu.

An samu kungiya kula da dabbobi ta Nijeriya da badakalar kudaden haraji na duti da kuma sauran kudaden haraji da suke karba.

An bai wa kungiyar umarnin dawo da Naira miliyan 1.1 na harajin dutin daga hannun ‘yan kwangila tare da kuma dawo da sama da Naira miliyan 19 na wasu kudade.

Yayin da majalisa ke karbar rahoton kwamitin, ta yi kira ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawa daban-daban da suka hada da EFCC, ICPC da FIRS da su kwato wadannan kudade.

Kwamitin ya kuma kara jaddada bukatar gaggauta bai wa shugabannin hukumomi damar nada masu binciken kudi daga waje, inda kuma ya bayar da shawarwarin yin gyara ga ka’idojin kudi ko wata takardar da sakataren gwamnatin tarayya zai bayar.

Mataimakin kakakin kajalisar, Rt. Hon. Benjamin Kalu, wanda ya jagoranci zaman majalisar tare da sauran ‘yan majalisa, sun yaba wad an majalisa Salam da sauran ‘yan kwamitin, bisa ga kwazon da suka nuna wajen samar da wannan cikakken rahoto.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fahimtar Sabon Tunani: Mene Ne Birnin Zamani Na Al’umma

Next Post

An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

Related

Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

58 minutes ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

12 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

14 hours ago
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
Labarai

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

15 hours ago
Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
Labarai

Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta

16 hours ago
Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

18 hours ago
Next Post
An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.