ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
majalisar kasa

Majalisar wakilai ta tarayya, ta tuhumi ma’aikatu da hukumomin gwamnati da badakalar kudade sama da Naira biliyan 103.8, wadanda suka yi daidai da dalar Amurka 950,912.05.  

Hakan na faruwa ne, yayin da majalisar ta bukaci hukumar EFCC da ICPC da sauran hukumomin da ke da alaka da su, da su bi ma’aikatu da hukumomin gwamnati, domin kwato kudaden tare da tura su asusun baitul-mali.

  • Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi
  • Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Wannan ya biyo bayan kudirin da dan majalisa mai wakiltar Bamidele Salam ya gabatar a ranar Talata, bisa sakamakon binciken da kwamitin kula da asusun gwamnati (PAC) ya yi, a yayin nazarin rahoton shekara-shekara na mai babban binciken kudi na shekarun da suka kare a ranar 31 ga Disambar 2019 da kuma 31 ga watan Disambar 2020, ciki har da binciken da ya shafi gazawar cikin gida da kuma gazawar gwamnati.

ADVERTISEMENT

Dangane da matakin tsayiwar daka na majalisar, shawarwarin da aka amince na nufin tabbatar da bin doka ta hanyar bayar da umarnin kwato kudaden jama’a da kuma sanya takunkumi a wurin da ya zama wajibi a sanya.

Daga cikin cibiyoyin da aka ayyana wajen yin binciken a 2019, akwai ma’aikatar harkokin wajen kasar, inda aka same tad a laifin kashe kudade ba tare da izini ba, kan aikin masaukin shugaban kasa a ofishin jakadancin Nijeriya da ke Habasha.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

Kwamitin ya nemi a mayar da sama da Naira miliyan 124, kusan dala 795,000 zuwa asusun gwamnatin tarayya, an kuma bayar da karin wasu kudade da suka hada da Naira miliyan 31.7 da dala 155,923.00, a matsayin wadanda aka kashe ba bisa ka’ida ba.

An umarci ma’aikatar da ta kwato Naira miliyan 49.4 da aka biya, domin yin gyaran ba tare da bin ka’idojin sayen kayayyakin ba. Kazalika, an raba Naira miliyan 9.2 ga jami’an ofishin jakadancin, ba tare da cikakkiyar shaida ba.

Haka nan kuma, an binciki bankin noma; kan basussuka kimanin Naira biliyan 75.6.

Kwamitin ya umarci hukumar da ta buga jerin sunayen wadanda ake bi bashi a akalla a jaridu guda uku na wannan kasa tare da yin kira ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawar da su kwato wadannan makudan kudade.

Haka nan, dole ne a kwato karin Naira miliyan 350; kana kuma a gabatar da shedu cikin kwanaki 90.

Sannan, an umarci hukumar kula da gidajen yari ta Nijeriya da ta dawo tare da tura Naira miliyan 7.47 na harajin da ba ta biya ba.

Haka zalika, an umarci hukumar kula da fitar da kayayyaki ta Nijeriya (NEPZA), da ta kwaso motoci takwas na hukumar tare da tabbatar da dawo da guda hudu da ma’aikatar masana’antu, kasuwanci da zuba jari ta rike ba bisa ka’ida ba.

An kuma bayyana (NEPZA) da laifin karkatar da sama da Naira miliyan 12 tare da sanya takunkumi ga jami’in da kula da harkokin kudi.

An gurfanar da Karamar Hukumar Kwali da ke babban birnin tarayya gaban kuliya, bisa zargin biyan kudi kimanin Naira miliyan 82 da aka raba wasu mutane su 105 da ba a san ko su wane ne ba.

Kazalika, an bukaci tsohon shugaban majalisa day a dawo da kudade zuwa asusun gwamnatin tarayya tare da wasu shaidun day a mika wa kwamitin.

Haka nan, an umarci hukumar kwastam ta Nijeriya da ta yi aiki tare da Akanta Janar na Tarayya, domin samar da cikakken jerin dukkannin abubuwan da aka bai wa asusun tarayya da wadanda ban a tarayya, don tabbatar da hakikanin kudaden da ake da su.

A hukumar samar da wutar lantarki ta karkara kuma, an bankado badakalar kudi sama da Naira biliyan 1.3.

Haka nan, an umarci tsohon manajan darakta da ya mayar da Naira miliyan 394 da ya batar kan ayyukan wutar lantarki da hukumar tattalin arziki ta kasa ta amince da shi.

Bugu da kari, akwai kuma kudaden da suka hada da Naira miliyan 4.2 da aka kashe wajen aiwatar da tallace-tallace, ba a kan ka’ida bad a kuma canza Naira miliyan 969 zuwa Yuro, shi ma ba a kan ka’ida ba, tare kuma da ba da shawarar daukar matakan ladabtarwa ga jami’an da ked a alhakin gudanar da ayyukansu.

An samu kungiya kula da dabbobi ta Nijeriya da badakalar kudaden haraji na duti da kuma sauran kudaden haraji da suke karba.

An bai wa kungiyar umarnin dawo da Naira miliyan 1.1 na harajin dutin daga hannun ‘yan kwangila tare da kuma dawo da sama da Naira miliyan 19 na wasu kudade.

Yayin da majalisa ke karbar rahoton kwamitin, ta yi kira ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawa daban-daban da suka hada da EFCC, ICPC da FIRS da su kwato wadannan kudade.

Kwamitin ya kuma kara jaddada bukatar gaggauta bai wa shugabannin hukumomi damar nada masu binciken kudi daga waje, inda kuma ya bayar da shawarwarin yin gyara ga ka’idojin kudi ko wata takardar da sakataren gwamnatin tarayya zai bayar.

Mataimakin kakakin kajalisar, Rt. Hon. Benjamin Kalu, wanda ya jagoranci zaman majalisar tare da sauran ‘yan majalisa, sun yaba wad an majalisa Salam da sauran ‘yan kwamitin, bisa ga kwazon da suka nuna wajen samar da wannan cikakken rahoto.

Majalisa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan
Majalisa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin
  • Sulaiman
    Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana
  • Sulaiman
    Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos
  • Sulaiman
    Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
Rahotonni

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026
Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza
Labarai

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

June 6, 2026
Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro
Manyan Labarai

Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

June 6, 2026
Next Post
An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

June 6, 2026
Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

June 6, 2026
Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.