• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 104.16 Ke Da Lambar Shaidar Dan Kasa – NIMC

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
‘Yan Nijeriya Miliyan 104.16 Ke Da Lambar Shaidar Dan Kasa – NIMC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 104.16 na da lambar shaidar zama dan kasa wato National Identification Numbers (NIN) zuwa ranar 31 ga watan Disamban shekarar 2023, kamar yadda bayanan da hukumar kula da shaidar dan kasa (NIMC) ta fitar.

A cewar bayanin, jihar Legas ce kan gaba wajen yawan mutanen da suke da lambar shaidar a fadin kasar nan da suka kai mutum miliyan 11.42. Yayin da kuma jihar Kano ta mara mata baya da yawan mutum 9.19 masu shaidar NIN.

  • Tinubu Ya Bada Umarnin Binciken Ma’aikatar Jin Kai Kan Zargin Karkatar Da Miliyan N585
  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Zaben Alex Otti A Matsayin Gwamnan Abia

Fitattu kuma manyan jihohi biyun a cewar bayanan da hukumar kididdiga ta kasa (NBS) su ne na gaba-gaba wajen samun lambar NIN tun lokacin da aka fara aikin samar da shaidar ga ‘yan Nijeriya.

Sauran jihohin da suka kasance na gaba-gaba wajen shiga sawun masu mallakar shaidar sun kunshi Kaduna mai miliyan 6.45; Ogun miliyan 4.40; Oyo miliyan 4.04; Katsina miliyan 3.54; birnin tarayya (FCT) mai miliyan 3.51; jihar Ribas miliyan 3.13; Delta miliyan 2.79 da kuma jihar Bauchi mai mutum miliyan 2.76 da ke da lambar shaidar zama cikakken dan kasa.

Kazalika, bayanan na NIMC na nuni da cewa jihohi 10 da suke matakin kasa kasa a samun shaidar NIN sun hada da Kwara mai miliyan 1.77; Akwa-Ibom mai miliyan 1.76; Kogi mai miliyan 1.73; Enugu mai miliyan 1.67; Yobe mai miliyan 1.65; Taraba mai miliyan 1.49; Kurus Ribas miliyan 1.19; Ekiti miliyan 1.02; Ebonyi mutum 839,506 ke da lambar yayin da jihar Bayelsa mutum 657,484 ke da lambar shaidar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

A gefe guda, sabowar darakta janar na NIMC, Injiniya Abisoye Coker-Odusote, ta bayyana cewar, hukumar ta himmatu da kara hanzarta wajen yin amfani da zamani wajen samar da shaidar tantancewa ga mutane a cikin manufofin shugaban kasa Bola Tinubu na sabunta fata ga ‘yan kasa.

A cewar Coker-Odusote, “NIMC ta maida hankali wajen ayyukan da ke gabanta na saukaka samar da shaidar kasa da suka kunshi lambar shaidar zama dan kasa NIM, da inshura, katin shaidar inshura e-ID, shaidar tantancewa gami da tantance bayanai da tabbatar da su. Ya kamata a lura a wannan zamanin na fasaha, shaidar tantancewa na gaba-gaba wajen saukaka gudanar da shirye-shirye.”

“Sannan, lambar tantancewa na bai wa gwamnati damar gabatar da tsare-tsare da shirye-shiryen ingantawa da bukasa rayuwar al’umma hadi da tsarin hidimar kudaden da za su taimaka wajen gudanar da lamura. Kazalika, tantancewar na taimaka wa gwamnati wajen gudanar da mulkin gaskiya da adalci hadi da shigo da kowa cikin sha’anin gudanar da mulki.”

Dangane da wahalhalun da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke sha wajen mallakar shaidar NIN kuwa, darakta-janar din ta bada tabbacin cewa za a shawo kan dukkanin matsalolin da suke akwai kuma za a yi kaddamar da bincike domin gano matsalolin da suke akwai da shawo kansu domin ‘yan Nijeriya su ke samun lambar a kan lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BVNNIMCNIN
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Maldives: Maldives Ta Samu Goyo Baya Daga Kasar Sin

Next Post

Gwamnatin Zimbabwe Ta Yabawa Ci Gaban Da Ake Samu A Masana’antar Samar Da Karafa Da Sin Ta Zubawa Jari

Related

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

37 minutes ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

2 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

4 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

5 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

6 hours ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

7 hours ago
Next Post
Gwamnatin Zimbabwe Ta Yabawa Ci Gaban Da Ake Samu A Masana’antar Samar Da Karafa Da Sin Ta Zubawa Jari

Gwamnatin Zimbabwe Ta Yabawa Ci Gaban Da Ake Samu A Masana’antar Samar Da Karafa Da Sin Ta Zubawa Jari

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.