• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 104.16 Ke Da Lambar Shaidar Dan Kasa – NIMC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
NIMC

Kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 104.16 na da lambar shaidar zama dan kasa wato National Identification Numbers (NIN) zuwa ranar 31 ga watan Disamban shekarar 2023, kamar yadda bayanan da hukumar kula da shaidar dan kasa (NIMC) ta fitar.

A cewar bayanin, jihar Legas ce kan gaba wajen yawan mutanen da suke da lambar shaidar a fadin kasar nan da suka kai mutum miliyan 11.42. Yayin da kuma jihar Kano ta mara mata baya da yawan mutum 9.19 masu shaidar NIN.

  • Tinubu Ya Bada Umarnin Binciken Ma’aikatar Jin Kai Kan Zargin Karkatar Da Miliyan N585
  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Zaben Alex Otti A Matsayin Gwamnan Abia

Fitattu kuma manyan jihohi biyun a cewar bayanan da hukumar kididdiga ta kasa (NBS) su ne na gaba-gaba wajen samun lambar NIN tun lokacin da aka fara aikin samar da shaidar ga ‘yan Nijeriya.

Sauran jihohin da suka kasance na gaba-gaba wajen shiga sawun masu mallakar shaidar sun kunshi Kaduna mai miliyan 6.45; Ogun miliyan 4.40; Oyo miliyan 4.04; Katsina miliyan 3.54; birnin tarayya (FCT) mai miliyan 3.51; jihar Ribas miliyan 3.13; Delta miliyan 2.79 da kuma jihar Bauchi mai mutum miliyan 2.76 da ke da lambar shaidar zama cikakken dan kasa.

Kazalika, bayanan na NIMC na nuni da cewa jihohi 10 da suke matakin kasa kasa a samun shaidar NIN sun hada da Kwara mai miliyan 1.77; Akwa-Ibom mai miliyan 1.76; Kogi mai miliyan 1.73; Enugu mai miliyan 1.67; Yobe mai miliyan 1.65; Taraba mai miliyan 1.49; Kurus Ribas miliyan 1.19; Ekiti miliyan 1.02; Ebonyi mutum 839,506 ke da lambar yayin da jihar Bayelsa mutum 657,484 ke da lambar shaidar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

A gefe guda, sabowar darakta janar na NIMC, Injiniya Abisoye Coker-Odusote, ta bayyana cewar, hukumar ta himmatu da kara hanzarta wajen yin amfani da zamani wajen samar da shaidar tantancewa ga mutane a cikin manufofin shugaban kasa Bola Tinubu na sabunta fata ga ‘yan kasa.

A cewar Coker-Odusote, “NIMC ta maida hankali wajen ayyukan da ke gabanta na saukaka samar da shaidar kasa da suka kunshi lambar shaidar zama dan kasa NIM, da inshura, katin shaidar inshura e-ID, shaidar tantancewa gami da tantance bayanai da tabbatar da su. Ya kamata a lura a wannan zamanin na fasaha, shaidar tantancewa na gaba-gaba wajen saukaka gudanar da shirye-shirye.”

“Sannan, lambar tantancewa na bai wa gwamnati damar gabatar da tsare-tsare da shirye-shiryen ingantawa da bukasa rayuwar al’umma hadi da tsarin hidimar kudaden da za su taimaka wajen gudanar da lamura. Kazalika, tantancewar na taimaka wa gwamnati wajen gudanar da mulkin gaskiya da adalci hadi da shigo da kowa cikin sha’anin gudanar da mulki.”

Dangane da wahalhalun da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke sha wajen mallakar shaidar NIN kuwa, darakta-janar din ta bada tabbacin cewa za a shawo kan dukkanin matsalolin da suke akwai kuma za a yi kaddamar da bincike domin gano matsalolin da suke akwai da shawo kansu domin ‘yan Nijeriya su ke samun lambar a kan lokaci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Gwamnatin Zimbabwe Ta Yabawa Ci Gaban Da Ake Samu A Masana’antar Samar Da Karafa Da Sin Ta Zubawa Jari

Gwamnatin Zimbabwe Ta Yabawa Ci Gaban Da Ake Samu A Masana’antar Samar Da Karafa Da Sin Ta Zubawa Jari

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.