ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 104.16 Ke Da Lambar Shaidar Dan Kasa – NIMC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NIMC

Kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 104.16 na da lambar shaidar zama dan kasa wato National Identification Numbers (NIN) zuwa ranar 31 ga watan Disamban shekarar 2023, kamar yadda bayanan da hukumar kula da shaidar dan kasa (NIMC) ta fitar.

A cewar bayanin, jihar Legas ce kan gaba wajen yawan mutanen da suke da lambar shaidar a fadin kasar nan da suka kai mutum miliyan 11.42. Yayin da kuma jihar Kano ta mara mata baya da yawan mutum 9.19 masu shaidar NIN.

  • Tinubu Ya Bada Umarnin Binciken Ma’aikatar Jin Kai Kan Zargin Karkatar Da Miliyan N585
  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Zaben Alex Otti A Matsayin Gwamnan Abia

Fitattu kuma manyan jihohi biyun a cewar bayanan da hukumar kididdiga ta kasa (NBS) su ne na gaba-gaba wajen samun lambar NIN tun lokacin da aka fara aikin samar da shaidar ga ‘yan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Sauran jihohin da suka kasance na gaba-gaba wajen shiga sawun masu mallakar shaidar sun kunshi Kaduna mai miliyan 6.45; Ogun miliyan 4.40; Oyo miliyan 4.04; Katsina miliyan 3.54; birnin tarayya (FCT) mai miliyan 3.51; jihar Ribas miliyan 3.13; Delta miliyan 2.79 da kuma jihar Bauchi mai mutum miliyan 2.76 da ke da lambar shaidar zama cikakken dan kasa.

Kazalika, bayanan na NIMC na nuni da cewa jihohi 10 da suke matakin kasa kasa a samun shaidar NIN sun hada da Kwara mai miliyan 1.77; Akwa-Ibom mai miliyan 1.76; Kogi mai miliyan 1.73; Enugu mai miliyan 1.67; Yobe mai miliyan 1.65; Taraba mai miliyan 1.49; Kurus Ribas miliyan 1.19; Ekiti miliyan 1.02; Ebonyi mutum 839,506 ke da lambar yayin da jihar Bayelsa mutum 657,484 ke da lambar shaidar.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

A gefe guda, sabowar darakta janar na NIMC, Injiniya Abisoye Coker-Odusote, ta bayyana cewar, hukumar ta himmatu da kara hanzarta wajen yin amfani da zamani wajen samar da shaidar tantancewa ga mutane a cikin manufofin shugaban kasa Bola Tinubu na sabunta fata ga ‘yan kasa.

A cewar Coker-Odusote, “NIMC ta maida hankali wajen ayyukan da ke gabanta na saukaka samar da shaidar kasa da suka kunshi lambar shaidar zama dan kasa NIM, da inshura, katin shaidar inshura e-ID, shaidar tantancewa gami da tantance bayanai da tabbatar da su. Ya kamata a lura a wannan zamanin na fasaha, shaidar tantancewa na gaba-gaba wajen saukaka gudanar da shirye-shirye.”

“Sannan, lambar tantancewa na bai wa gwamnati damar gabatar da tsare-tsare da shirye-shiryen ingantawa da bukasa rayuwar al’umma hadi da tsarin hidimar kudaden da za su taimaka wajen gudanar da lamura. Kazalika, tantancewar na taimaka wa gwamnati wajen gudanar da mulkin gaskiya da adalci hadi da shigo da kowa cikin sha’anin gudanar da mulki.”

Dangane da wahalhalun da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke sha wajen mallakar shaidar NIN kuwa, darakta-janar din ta bada tabbacin cewa za a shawo kan dukkanin matsalolin da suke akwai kuma za a yi kaddamar da bincike domin gano matsalolin da suke akwai da shawo kansu domin ‘yan Nijeriya su ke samun lambar a kan lokaci.

NIMC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Gwamnatin Zimbabwe Ta Yabawa Ci Gaban Da Ake Samu A Masana’antar Samar Da Karafa Da Sin Ta Zubawa Jari

Gwamnatin Zimbabwe Ta Yabawa Ci Gaban Da Ake Samu A Masana’antar Samar Da Karafa Da Sin Ta Zubawa Jari

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.