ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 104.16 Ke Da Lambar Shaidar Dan Kasa – NIMC

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
NIMC

Kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 104.16 na da lambar shaidar zama dan kasa wato National Identification Numbers (NIN) zuwa ranar 31 ga watan Disamban shekarar 2023, kamar yadda bayanan da hukumar kula da shaidar dan kasa (NIMC) ta fitar.

A cewar bayanin, jihar Legas ce kan gaba wajen yawan mutanen da suke da lambar shaidar a fadin kasar nan da suka kai mutum miliyan 11.42. Yayin da kuma jihar Kano ta mara mata baya da yawan mutum 9.19 masu shaidar NIN.

  • Tinubu Ya Bada Umarnin Binciken Ma’aikatar Jin Kai Kan Zargin Karkatar Da Miliyan N585
  • Kotun Koli Ta Tabbatar Da Zaben Alex Otti A Matsayin Gwamnan Abia

Fitattu kuma manyan jihohi biyun a cewar bayanan da hukumar kididdiga ta kasa (NBS) su ne na gaba-gaba wajen samun lambar NIN tun lokacin da aka fara aikin samar da shaidar ga ‘yan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Sauran jihohin da suka kasance na gaba-gaba wajen shiga sawun masu mallakar shaidar sun kunshi Kaduna mai miliyan 6.45; Ogun miliyan 4.40; Oyo miliyan 4.04; Katsina miliyan 3.54; birnin tarayya (FCT) mai miliyan 3.51; jihar Ribas miliyan 3.13; Delta miliyan 2.79 da kuma jihar Bauchi mai mutum miliyan 2.76 da ke da lambar shaidar zama cikakken dan kasa.

Kazalika, bayanan na NIMC na nuni da cewa jihohi 10 da suke matakin kasa kasa a samun shaidar NIN sun hada da Kwara mai miliyan 1.77; Akwa-Ibom mai miliyan 1.76; Kogi mai miliyan 1.73; Enugu mai miliyan 1.67; Yobe mai miliyan 1.65; Taraba mai miliyan 1.49; Kurus Ribas miliyan 1.19; Ekiti miliyan 1.02; Ebonyi mutum 839,506 ke da lambar yayin da jihar Bayelsa mutum 657,484 ke da lambar shaidar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A gefe guda, sabowar darakta janar na NIMC, Injiniya Abisoye Coker-Odusote, ta bayyana cewar, hukumar ta himmatu da kara hanzarta wajen yin amfani da zamani wajen samar da shaidar tantancewa ga mutane a cikin manufofin shugaban kasa Bola Tinubu na sabunta fata ga ‘yan kasa.

A cewar Coker-Odusote, “NIMC ta maida hankali wajen ayyukan da ke gabanta na saukaka samar da shaidar kasa da suka kunshi lambar shaidar zama dan kasa NIM, da inshura, katin shaidar inshura e-ID, shaidar tantancewa gami da tantance bayanai da tabbatar da su. Ya kamata a lura a wannan zamanin na fasaha, shaidar tantancewa na gaba-gaba wajen saukaka gudanar da shirye-shirye.”

“Sannan, lambar tantancewa na bai wa gwamnati damar gabatar da tsare-tsare da shirye-shiryen ingantawa da bukasa rayuwar al’umma hadi da tsarin hidimar kudaden da za su taimaka wajen gudanar da lamura. Kazalika, tantancewar na taimaka wa gwamnati wajen gudanar da mulkin gaskiya da adalci hadi da shigo da kowa cikin sha’anin gudanar da mulki.”

Dangane da wahalhalun da miliyoyin ‘yan Nijeriya ke sha wajen mallakar shaidar NIN kuwa, darakta-janar din ta bada tabbacin cewa za a shawo kan dukkanin matsalolin da suke akwai kuma za a yi kaddamar da bincike domin gano matsalolin da suke akwai da shawo kansu domin ‘yan Nijeriya su ke samun lambar a kan lokaci.

NIMC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Zimbabwe Ta Yabawa Ci Gaban Da Ake Samu A Masana’antar Samar Da Karafa Da Sin Ta Zubawa Jari

Gwamnatin Zimbabwe Ta Yabawa Ci Gaban Da Ake Samu A Masana’antar Samar Da Karafa Da Sin Ta Zubawa Jari

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.