• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
9 months ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
‘Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya na iya rasa burinta na yunkurin zuba hannun jarin kamfanoni masu zaman kansu da hasashen cimma nasarar kyautata sadarwa nan da 2025, yayin da ‘yan Nijeriya Miliyan 136 ba su da damar amfani ko mu’amala da yanar gizo (intanet).

 

Wannan na zuwa ne yayin da bayanan da bangaren sadarwar Nijeriya ke nuni da irin wagegen gibin da ake samu a bangaren fasaha a tsakanin arewa da kudancin Nijeriya.

  • Kudaden ‘Yan Majalisa: Wa Za A Gaskata Tsakanin Hukumar Albashi Da Kawu Sumaila?
  • Tinubu Ya Amince Da Karin Albashi Da Kashi 300 Ga Alkalan Nijeriya

Kaso 44.6 na ‘yan Nijeriya wadanda galibinsu daga arewaci, walau ko ba su da karfin sadarwar wayar salulu gaba ki daya ko kuma shan wahalar samu.

 

Labarai Masu Nasaba

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Duba da yawan kiyasin ‘yan Nijeriya miliyan 220, bayanai na nuni da cewa, kaso 38 na ‘yan kasar nan kawai ke iya samun damar mu’amala da yanar gizo, hakan na nuni da cewa wasu kimanin mutum miliyan 136 har yanzu na fama da wahalar rashin samar damar mu’amala da yanar gizo.

 

Yayin da aka kiyasce yawan buga wayar da ake yi a kasar ya kai kaso 101.2 a zangon farko, inda binciken da masu ma’aikata ya nuna kaso 61 cikin dari na mutanen da ke zama a yankunan karkara da yawanci suka fito daga arewa ba su da samun irin wannan damar.

 

A shekarar da ta gabata, Nijeriya ta samu maki 0.38 a kiddigar ingancin fasahar sadarwa inda ta samu hawa na 88 a cikin kasashe 117 da Statista da hadin guiwar Surfshark suka gudanar da bincike a cikinsu.

 

A hakan ma adadin ya karu idan aka kwanta da shekarar baya da ta samu maki 0.34. Binciken na duba bangarori biyar da suka hada da saukin samun yanar gizo, ingancinsa, tsarin yanar gizo mai kyau, tsaron yanar gizo, nagartar da kwarin fasahar sadarwa ga ‘yan kasa.

 

Ita kuma a bangarenta, kungiyar bangaren sadarwa na kasa da kasa (ITU) ta shelanta Nijeriya a matsayin wacce ta ke da kaso 71 a bangaren daidaito Shari’a da kyakkyawar tsarin zuwa matakin G5.

 

Babban gibin da ake da shi a bangaren sadarwa ta yanar gizo ko karfin sadarwar kiran waya ya kara tabbata ne da bayanan hukumar kididdiga ta kasa (NBS).

 

Bayanan ya nuna cewa mutum miliyan 113.8 da suke amfani da wayar salula suna kudanci ne, yayin da mutum miliyan 104.5 suke arewa. Kuma, da yiyuwar gibin da ake da shi zai cigaba da karuwa lura da jan kafa da ake yi wajen aiwatar da tsarin karfin sadarwa na Broadband Plan daga 2020 zuwa 2025.

 

Bincike ya nuna cewa gine-ginen kamfanonin sadarwa daban-daban ne suka gamu da hare-haren ‘yan Boko Haram a jihohin arewa shekarun baya, kuma har yanzu ba a gyara su ba. Hakan na kara janyo koma baya ga ayyukan kamfanonin sadarwa.

 

A kwanakin nan da suka wuce an ga yadda masu zanga-zangar tsadar rayuwa suka buga wasoso da lalata sabon tashar fasahar sadarwa na hukumar sadarwa ta kasa (NCC) da ke Kano.

 

Kan hanyoyin da za a kyautata sadarwa a Nijeriya, kamfanoni daban daban sun yi yunkurin taimaka wa Nijeriya wajen hada wayoyin da za su janyo karfin sadarwa a kananan hukumomi sama da 700 amma haka ba ta cimma ruwa ba.

 

Gwamnatin tarayya ya sake wani yunkuri ta hannun shirin 224 LG na kafa layukan da wayoyin sadarwa, amma an fuskantar daina amfani da 2G da 3G domin fadadawa zuwa matakin 4G da 5G.

 

Kididdiga ta NCC ta nuna cewa 2G, wanda ke da iyakacin aiki, yana da kashi 56.97 cikin 100 na shigar da shi, wanda hakan ke nufin har yanzu mutane da yawa suna kan hanyar sadarwar, musamman a yankunan karkara; don haka da yawa ba sa iya yin abubuwa da yawa ta hanyar dijital da ake hasashen kaiwa ba.

 

A cewar mai kula da harkokin sadarwa, 3G yana da kashi 9.04 bisa 100, 4G, kashi 32.74 cikin 100 kuma har yanzu yana iyakance ga manyan birane. Kusan shekaru biyu da kaddamar da shi, 5G ya ga kashi 1.24 cikin ɗari kawai ya shiga. Manazarta masana’antu sun ce rashin saka hannun jari ya kawo cikas wajen fitar da jarin ya kawo cikas ga bullowar hanyoyin sadarwa a sabbin shafuka da wurare.

 

Yayin da hukumar ta NNBP ta ayyana bukatar rufe kashi 80 cikin 100 na gungu 114 da ba a yi amfani da su ba a kasar nan a karshen shekarar da ta gabata, hakan bai samu ba kamar yadda hanyoyin sadarwa na metro fiber a halin yanzu ke da kasa da kashi 25 cikin 100 na jimillar tazarar fiber. A kasar da ke da tarin yawa a Legas, Abuja da Fatakwal, yayin da sauran yankunan ba a yi musu hidima ba ko kuma ba a yi musu hidima ba’

 

Samun hanyoyin sadarwa na fiber a tsakanin kilomita biyar a halin yanzu ya kai kusan kashi 39 cikin 100, inda ya kai kashi 85 cikin 100 a Legas sannan kuma bai kai kashi 12 cikin dari a jihar Jigawa ba.

 

A cewar NNBP, ya zuwa shekarar 2023, ana sa ran Nijeriya za ta hade ta hanyar fiber, kashi 70 cikin 100 na manyan makarantu, kashi 30 na sakandare da kuma kashi 15 na makarantun firamare.

 

A daidai wannan lokacin, ya kamata a hada kashi 80 na manyan asibitoci a kowace karamar hukuma da cibiyoyin kiwon lafiya na tarayya. Amma kuma ba a cimma nasara ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci gaban AfirkaFasahar 5gFasahar Zamani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan ‘Yancin Kananan Hukumomi – PDP

Next Post

Muna Gyara Da Gina Sabbin Makarantu 290 A Zamfara – Gwamna Dauda

Related

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

4 weeks ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

2 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

2 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

3 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

7 months ago
Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk

7 months ago
Next Post
Muna Gyara Da Gina Sabbin Makarantu 290 A Zamfara – Gwamna Dauda

Muna Gyara Da Gina Sabbin Makarantu 290 A Zamfara - Gwamna Dauda

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.