ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Gyara Da Gina Sabbin Makarantu 290 A Zamfara – Gwamna Dauda

by Leadership Hausa
2 years ago
makarantu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa suna gyara tare da gina wasu sabbin makarantu 290 a fadin jihar domin bunkasa ilimi.

Gwamnan ya kuma bayyana Kwalejin Ilimi ta Tarayya ta ƙere-ƙere da ke jihar a matsayin wani ginshiƙin samar da ƙwararrun malamai a makarantun gwamnati a Zamfara.

Majalisar Gudanarwa ta Kwalejin Ƙere-ƙere ta Tarayya (Technical) da ke Gusau, ta kai wa Gwamna Lawal ziyarar ban-girma a gidan gwamnatin Jihar Zamfara da ke Gusau a ranar Laraba.

ADVERTISEMENT

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, sun kai ziyarar ban-girma ne domin fahimtar juna da kuma inganta haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar da majalisar FCET ta Gusau.

makarantu

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya yi maraba da mambobin majalisar gudanarwar tare da jaddada buƙatar bai wa Kwalejin Ilimi ta Tarayya duk kulawar da ta dace.

“Ina so in fara da cewa al’ummar Jihar Zamfara sun daɗe suna cin gajiyar Kwalejin Ilimi ta Tarayya, Gusau. In ma taƙaice zance: ‘yan uwana mata kusan biyar ne suka yi karatu a FCET.

“Kamar yadda shugaban ya bayyana, a fannin ilimi, Jihar Zamfara ta kasance a baya tsawon shekaru. Gogayya muke yi da Yobe a matsayi na ƙarshe.

“A shekarar da ta gabata, na kafa dokar ta-ɓaci a ɓangaren ilimi na Zamfara saboda ƙalubalen da ake fuskanta a fannin. Abin takaici, a cikin shekaru uku da suka gabata, gwamnatin da ta shuɗe ta kasa biyan kuɗin jarrabawar NECO da WAEC na ɗalibai. Duk da haka, mun biya bashin, wanda yanzu ya zama tarihi.

“Kwanan nan, mai yiwuwa ka karanta a labarai game da ƙwazon da ɗalibanmu suka yi a jarrabawar ɗalibai masu hazaƙa na NECO. Jiharmu ta Zamfara ta zama jihar da ta yi zarra a duk faɗin Arewa kuma ta biyu a faɗin ƙasar nan.

“Mun himmatu wajen ganin kowane yaro ya samu ingantaccen ilimi. A yanzu haka muna gyara da gina makarantu sama da 290 a faɗin jihar nan.

“Matakan da muke ɗauka sun haɗa da samar da ingantattun kayan karatu da kuma ba da horo ga malaman mu. A cikin wannan yunƙurin, FCET tana taka rawar gani yayin da muke son haɓaka iyawa da ingancin malaman mu. Don haka za mu yi aiki kafaɗa-da-kafaɗa domin gyara harkar ilimi a Jihar Zamfara.

Tun da farko, Farfesa Muhammad Bashir Nuhu, shugaban majalisar gudanarwa na Kwalejin Ilimi ta Tarayya (Technical), ya yaba wa gwamnan bisa ba da fifiko ga ilimi a cikin ajandar gwamnatinsa.

makarantu

Ya ce, “Mu ne majalisar gudanarwar babbar kwalejin FCET. Ana ɗaukarta da daraja domin ita kaɗai ce irinta a faɗin tarayyar ƙasar a lokacin da aka kafa ta. Lokacin da aka kafa ta, an yi ta hassada da yawa game da dalilin da ya sa aka kafa ta a Zamfara. Daga baya na gane cewa wannan ya faru ne saboda jihar Zamfara na ɗaya daga cikin jihohin da suka fi fama da matsalar ilimi.

“A yau, mun zo nan ne saboda gwamnatin ku ta ayyana dokar ta-ɓaci a fannin ilimi na jihar da kuma kyawawan matakan da kuke ɗauka na inganta fannin.

“Muna yaba muku da ƙoƙarinku, kuma muna so mu yi amfani da wannan dama wajen yaba wa uwargidan gwamna Hajiya Huriyya Dauda, ​​wadda ta ɗauki nauyin ɗalibai 20 a ƙwalejin tare da bai wa ɗalibai uku na farko da suka yaye na’ura mai kwakwalwa guda uku.”

makarantu
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Sin Ta Harba Gungun Taurarin Dan Adam Na Binciken Doron Kasa

Sin Ta Harba Gungun Taurarin Dan Adam Na Binciken Doron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.