ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Gyara Da Gina Sabbin Makarantu 290 A Zamfara – Gwamna Dauda

by Leadership Hausa
2 years ago
makarantu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa suna gyara tare da gina wasu sabbin makarantu 290 a fadin jihar domin bunkasa ilimi.

Gwamnan ya kuma bayyana Kwalejin Ilimi ta Tarayya ta ƙere-ƙere da ke jihar a matsayin wani ginshiƙin samar da ƙwararrun malamai a makarantun gwamnati a Zamfara.

Majalisar Gudanarwa ta Kwalejin Ƙere-ƙere ta Tarayya (Technical) da ke Gusau, ta kai wa Gwamna Lawal ziyarar ban-girma a gidan gwamnatin Jihar Zamfara da ke Gusau a ranar Laraba.

ADVERTISEMENT

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, sun kai ziyarar ban-girma ne domin fahimtar juna da kuma inganta haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar da majalisar FCET ta Gusau.

makarantu

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya yi maraba da mambobin majalisar gudanarwar tare da jaddada buƙatar bai wa Kwalejin Ilimi ta Tarayya duk kulawar da ta dace.

“Ina so in fara da cewa al’ummar Jihar Zamfara sun daɗe suna cin gajiyar Kwalejin Ilimi ta Tarayya, Gusau. In ma taƙaice zance: ‘yan uwana mata kusan biyar ne suka yi karatu a FCET.

“Kamar yadda shugaban ya bayyana, a fannin ilimi, Jihar Zamfara ta kasance a baya tsawon shekaru. Gogayya muke yi da Yobe a matsayi na ƙarshe.

“A shekarar da ta gabata, na kafa dokar ta-ɓaci a ɓangaren ilimi na Zamfara saboda ƙalubalen da ake fuskanta a fannin. Abin takaici, a cikin shekaru uku da suka gabata, gwamnatin da ta shuɗe ta kasa biyan kuɗin jarrabawar NECO da WAEC na ɗalibai. Duk da haka, mun biya bashin, wanda yanzu ya zama tarihi.

“Kwanan nan, mai yiwuwa ka karanta a labarai game da ƙwazon da ɗalibanmu suka yi a jarrabawar ɗalibai masu hazaƙa na NECO. Jiharmu ta Zamfara ta zama jihar da ta yi zarra a duk faɗin Arewa kuma ta biyu a faɗin ƙasar nan.

“Mun himmatu wajen ganin kowane yaro ya samu ingantaccen ilimi. A yanzu haka muna gyara da gina makarantu sama da 290 a faɗin jihar nan.

“Matakan da muke ɗauka sun haɗa da samar da ingantattun kayan karatu da kuma ba da horo ga malaman mu. A cikin wannan yunƙurin, FCET tana taka rawar gani yayin da muke son haɓaka iyawa da ingancin malaman mu. Don haka za mu yi aiki kafaɗa-da-kafaɗa domin gyara harkar ilimi a Jihar Zamfara.

Tun da farko, Farfesa Muhammad Bashir Nuhu, shugaban majalisar gudanarwa na Kwalejin Ilimi ta Tarayya (Technical), ya yaba wa gwamnan bisa ba da fifiko ga ilimi a cikin ajandar gwamnatinsa.

makarantu

Ya ce, “Mu ne majalisar gudanarwar babbar kwalejin FCET. Ana ɗaukarta da daraja domin ita kaɗai ce irinta a faɗin tarayyar ƙasar a lokacin da aka kafa ta. Lokacin da aka kafa ta, an yi ta hassada da yawa game da dalilin da ya sa aka kafa ta a Zamfara. Daga baya na gane cewa wannan ya faru ne saboda jihar Zamfara na ɗaya daga cikin jihohin da suka fi fama da matsalar ilimi.

“A yau, mun zo nan ne saboda gwamnatin ku ta ayyana dokar ta-ɓaci a fannin ilimi na jihar da kuma kyawawan matakan da kuke ɗauka na inganta fannin.

“Muna yaba muku da ƙoƙarinku, kuma muna so mu yi amfani da wannan dama wajen yaba wa uwargidan gwamna Hajiya Huriyya Dauda, ​​wadda ta ɗauki nauyin ɗalibai 20 a ƙwalejin tare da bai wa ɗalibai uku na farko da suka yaye na’ura mai kwakwalwa guda uku.”

makarantu
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Sin Ta Harba Gungun Taurarin Dan Adam Na Binciken Doron Kasa

Sin Ta Harba Gungun Taurarin Dan Adam Na Binciken Doron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
makarantu

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
makarantu

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
makarantu

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.