• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Gyara Da Gina Sabbin Makarantu 290 A Zamfara – Gwamna Dauda

by Leadership Hausa
11 months ago
in Ilimi
0
Muna Gyara Da Gina Sabbin Makarantu 290 A Zamfara – Gwamna Dauda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa suna gyara tare da gina wasu sabbin makarantu 290 a fadin jihar domin bunkasa ilimi.

Gwamnan ya kuma bayyana Kwalejin Ilimi ta Tarayya ta ƙere-ƙere da ke jihar a matsayin wani ginshiƙin samar da ƙwararrun malamai a makarantun gwamnati a Zamfara.

Majalisar Gudanarwa ta Kwalejin Ƙere-ƙere ta Tarayya (Technical) da ke Gusau, ta kai wa Gwamna Lawal ziyarar ban-girma a gidan gwamnatin Jihar Zamfara da ke Gusau a ranar Laraba.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, sun kai ziyarar ban-girma ne domin fahimtar juna da kuma inganta haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin jihar da majalisar FCET ta Gusau.

makarantu

Labarai Masu Nasaba

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya yi maraba da mambobin majalisar gudanarwar tare da jaddada buƙatar bai wa Kwalejin Ilimi ta Tarayya duk kulawar da ta dace.

“Ina so in fara da cewa al’ummar Jihar Zamfara sun daɗe suna cin gajiyar Kwalejin Ilimi ta Tarayya, Gusau. In ma taƙaice zance: ‘yan uwana mata kusan biyar ne suka yi karatu a FCET.

“Kamar yadda shugaban ya bayyana, a fannin ilimi, Jihar Zamfara ta kasance a baya tsawon shekaru. Gogayya muke yi da Yobe a matsayi na ƙarshe.

“A shekarar da ta gabata, na kafa dokar ta-ɓaci a ɓangaren ilimi na Zamfara saboda ƙalubalen da ake fuskanta a fannin. Abin takaici, a cikin shekaru uku da suka gabata, gwamnatin da ta shuɗe ta kasa biyan kuɗin jarrabawar NECO da WAEC na ɗalibai. Duk da haka, mun biya bashin, wanda yanzu ya zama tarihi.

“Kwanan nan, mai yiwuwa ka karanta a labarai game da ƙwazon da ɗalibanmu suka yi a jarrabawar ɗalibai masu hazaƙa na NECO. Jiharmu ta Zamfara ta zama jihar da ta yi zarra a duk faɗin Arewa kuma ta biyu a faɗin ƙasar nan.

“Mun himmatu wajen ganin kowane yaro ya samu ingantaccen ilimi. A yanzu haka muna gyara da gina makarantu sama da 290 a faɗin jihar nan.

“Matakan da muke ɗauka sun haɗa da samar da ingantattun kayan karatu da kuma ba da horo ga malaman mu. A cikin wannan yunƙurin, FCET tana taka rawar gani yayin da muke son haɓaka iyawa da ingancin malaman mu. Don haka za mu yi aiki kafaɗa-da-kafaɗa domin gyara harkar ilimi a Jihar Zamfara.

Tun da farko, Farfesa Muhammad Bashir Nuhu, shugaban majalisar gudanarwa na Kwalejin Ilimi ta Tarayya (Technical), ya yaba wa gwamnan bisa ba da fifiko ga ilimi a cikin ajandar gwamnatinsa.

makarantu

Ya ce, “Mu ne majalisar gudanarwar babbar kwalejin FCET. Ana ɗaukarta da daraja domin ita kaɗai ce irinta a faɗin tarayyar ƙasar a lokacin da aka kafa ta. Lokacin da aka kafa ta, an yi ta hassada da yawa game da dalilin da ya sa aka kafa ta a Zamfara. Daga baya na gane cewa wannan ya faru ne saboda jihar Zamfara na ɗaya daga cikin jihohin da suka fi fama da matsalar ilimi.

“A yau, mun zo nan ne saboda gwamnatin ku ta ayyana dokar ta-ɓaci a fannin ilimi na jihar da kuma kyawawan matakan da kuke ɗauka na inganta fannin.

“Muna yaba muku da ƙoƙarinku, kuma muna so mu yi amfani da wannan dama wajen yaba wa uwargidan gwamna Hajiya Huriyya Dauda, ​​wadda ta ɗauki nauyin ɗalibai 20 a ƙwalejin tare da bai wa ɗalibai uku na farko da suka yaye na’ura mai kwakwalwa guda uku.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna Dauda LawalIlimiKwalejiƘere-ƙereTarayyaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Nijeriya Miliyan 136 Ba Su Samun Damar Amfani Da Intanet

Next Post

Sin Ta Harba Gungun Taurarin Dan Adam Na Binciken Doron Kasa

Related

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
Ilimi

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

4 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

5 days ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

2 weeks ago
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
Ilimi

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

3 weeks ago
Next Post
Sin Ta Harba Gungun Taurarin Dan Adam Na Binciken Doron Kasa

Sin Ta Harba Gungun Taurarin Dan Adam Na Binciken Doron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.