• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Mu Hankalta, Wasan Kwaikwayo ‘Yan Siyasa Ke Yi Da Mu, In Ji Matasan Arewa A Kudu

byyahuzajere
3 years ago
inLabarai
0
Yan Nijeriya

Shugaban Matasan Arewa A Kudu, Alhaji Ibrahim Ya'u Galadanci

Abubuwan da ke faruwa a ƙasar nan sun nuna ƙarara ‘yan siyasarmu ba komai suke yi ba illa wasan kwaikwayo da rayukan mu ‘Yan Nijeriya, don haka kowa ya san alƙiblar da zai bi. Shugaban Gamayyar Matasan Arewa a Kudancin Nijeriya da ke Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya furta haka domin nuna damuwarsa kan zubar da jini da nakasta ‘yan arewa da ake ci gaba da yi a kullu yaumin.

  • 2023: Duk Sanatocin Bauchi Masu Ci Babu Mai Komawa Sun Sha Kaye A Mazabunsu
  • 2023: Jm’iyyar APC Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugabancin Nijeriya

Ya bayyana haka ne yayin da yake kokawa a wata sanarwa ga manema labarai inda ya yi bayanin cewa, “yadda shugabannin siyasar ƙasarmu Nijeriya suke cutar da al’ummar ƙasar nan wanda duk mai hankali da hangen nesa ya kamata ya ba wa kansa amsa, abin dubawa ne. Domin yadda ‘yan siyasa suke wasan kwaikwayo da ‘Yan Nijeriya ya zama wajibi ne kowa ya san inda ya dosa, sun bari ana ta asarar rayuka ba-ji-ba-gani amma siyasarsu kawai suka sa gaba. Ɗan arewa ya zama Ɗanbora, an ware shi a ƙasar nan bai da wani kataɓus. A kashe shi, a tafi da iyalinsa, a sace dukiyarsa duk babu mai nuna damuwa a cikin waɗannan ‘yan siyasar illa sha’anin gabansu kawai. Waɗanne irin mutane ne muke da su a matsayin shugabanni? Jinin ɗan arewa yana kwarara amma kowa siyasarsa kawai ya sa gaba.

“Duk wani babba da ya ce yana tare da talaka ya zama abin ƙyama a gun ɓata-garin shugabannin Nijeriya, ina jami’an tsaronmu masu kishin Nijeriya? Kuna ina ne ake yi wa ƙannenku da iyayenku kisan gilla babu wani shugaban da ke yin magana? Dan haka muna kira ga matasa da sauran ƙungiyoyin ‘yan arewa da mu nema wa kanmu mafita tun kafin lokaci ya ƙure mana.” In ji shi.

Alhaji Ibrahim ya kuma nuna damuwa a kan rashin ‘yanto mutanen da aka sace ana garkuwa da su waɗanda ya ce Allah kaɗai ya san irin azabar da suke sha a hannun ‘yan ta’adda.

Ya ƙara da cewa, “ina mutanen da aka sace a jirgin ƙasan da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna, tambaya a nan ita ce idan kwangila waɗansu suka karɓa don a yi mana wannan kisan mummuƙe a fito fili a yi mana bayani, domin yadda ɗan arewa ya zama a ƙasar nan a yau dabba ta fishi daraja, cin zarafin ya yi yawa mutaƙar gaske. Don haka muna mkira ga ‘Yan Nijeriya musamman ‘yan arewa mu san su waye za mu mara wa baya da za su zama mana tudun tsira a zaɓen 2023, idan ba haka ba, za mu ci gaba da zama jiya-i-yau kuma ba za mu yarda da hakan ba.” Ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

 

 

 

ShareTweetSendShare
yahuzajere

yahuzajere

Related

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

4 hours ago
Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga
Labarai

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

6 hours ago
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

7 hours ago
Next Post
Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Na Kasar Sin Kusan Dubu 50 Sun Shiga Ayyukan Kare Zaman Lafiya Na MDD

Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Na Kasar Sin Kusan Dubu 50 Sun Shiga Ayyukan Kare Zaman Lafiya Na MDD

LABARAI MASU NASABA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

October 7, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

October 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.