ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Mu Hankalta, Wasan Kwaikwayo ‘Yan Siyasa Ke Yi Da Mu, In Ji Matasan Arewa A Kudu

by yahuzajere
4 years ago
Yan Nijeriya

Shugaban Matasan Arewa A Kudu, Alhaji Ibrahim Ya'u Galadanci

Abubuwan da ke faruwa a ƙasar nan sun nuna ƙarara ‘yan siyasarmu ba komai suke yi ba illa wasan kwaikwayo da rayukan mu ‘Yan Nijeriya, don haka kowa ya san alƙiblar da zai bi. Shugaban Gamayyar Matasan Arewa a Kudancin Nijeriya da ke Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya furta haka domin nuna damuwarsa kan zubar da jini da nakasta ‘yan arewa da ake ci gaba da yi a kullu yaumin.

  • 2023: Duk Sanatocin Bauchi Masu Ci Babu Mai Komawa Sun Sha Kaye A Mazabunsu
  • 2023: Jm’iyyar APC Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugabancin Nijeriya

Ya bayyana haka ne yayin da yake kokawa a wata sanarwa ga manema labarai inda ya yi bayanin cewa, “yadda shugabannin siyasar ƙasarmu Nijeriya suke cutar da al’ummar ƙasar nan wanda duk mai hankali da hangen nesa ya kamata ya ba wa kansa amsa, abin dubawa ne. Domin yadda ‘yan siyasa suke wasan kwaikwayo da ‘Yan Nijeriya ya zama wajibi ne kowa ya san inda ya dosa, sun bari ana ta asarar rayuka ba-ji-ba-gani amma siyasarsu kawai suka sa gaba. Ɗan arewa ya zama Ɗanbora, an ware shi a ƙasar nan bai da wani kataɓus. A kashe shi, a tafi da iyalinsa, a sace dukiyarsa duk babu mai nuna damuwa a cikin waɗannan ‘yan siyasar illa sha’anin gabansu kawai. Waɗanne irin mutane ne muke da su a matsayin shugabanni? Jinin ɗan arewa yana kwarara amma kowa siyasarsa kawai ya sa gaba.

“Duk wani babba da ya ce yana tare da talaka ya zama abin ƙyama a gun ɓata-garin shugabannin Nijeriya, ina jami’an tsaronmu masu kishin Nijeriya? Kuna ina ne ake yi wa ƙannenku da iyayenku kisan gilla babu wani shugaban da ke yin magana? Dan haka muna kira ga matasa da sauran ƙungiyoyin ‘yan arewa da mu nema wa kanmu mafita tun kafin lokaci ya ƙure mana.” In ji shi.

ADVERTISEMENT

Alhaji Ibrahim ya kuma nuna damuwa a kan rashin ‘yanto mutanen da aka sace ana garkuwa da su waɗanda ya ce Allah kaɗai ya san irin azabar da suke sha a hannun ‘yan ta’adda.

Ya ƙara da cewa, “ina mutanen da aka sace a jirgin ƙasan da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna, tambaya a nan ita ce idan kwangila waɗansu suka karɓa don a yi mana wannan kisan mummuƙe a fito fili a yi mana bayani, domin yadda ɗan arewa ya zama a ƙasar nan a yau dabba ta fishi daraja, cin zarafin ya yi yawa mutaƙar gaske. Don haka muna mkira ga ‘Yan Nijeriya musamman ‘yan arewa mu san su waye za mu mara wa baya da za su zama mana tudun tsira a zaɓen 2023, idan ba haka ba, za mu ci gaba da zama jiya-i-yau kuma ba za mu yarda da hakan ba.” Ya bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

 

 

 

Yan Nijeriya
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Labarai

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Next Post
Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Na Kasar Sin Kusan Dubu 50 Sun Shiga Ayyukan Kare Zaman Lafiya Na MDD

Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Na Kasar Sin Kusan Dubu 50 Sun Shiga Ayyukan Kare Zaman Lafiya Na MDD

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.