ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Mu Hankalta, Wasan Kwaikwayo ‘Yan Siyasa Ke Yi Da Mu, In Ji Matasan Arewa A Kudu

by yahuzajere
4 years ago
Yan Nijeriya

Shugaban Matasan Arewa A Kudu, Alhaji Ibrahim Ya'u Galadanci

Abubuwan da ke faruwa a ƙasar nan sun nuna ƙarara ‘yan siyasarmu ba komai suke yi ba illa wasan kwaikwayo da rayukan mu ‘Yan Nijeriya, don haka kowa ya san alƙiblar da zai bi. Shugaban Gamayyar Matasan Arewa a Kudancin Nijeriya da ke Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya furta haka domin nuna damuwarsa kan zubar da jini da nakasta ‘yan arewa da ake ci gaba da yi a kullu yaumin.

  • 2023: Duk Sanatocin Bauchi Masu Ci Babu Mai Komawa Sun Sha Kaye A Mazabunsu
  • 2023: Jm’iyyar APC Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugabancin Nijeriya

Ya bayyana haka ne yayin da yake kokawa a wata sanarwa ga manema labarai inda ya yi bayanin cewa, “yadda shugabannin siyasar ƙasarmu Nijeriya suke cutar da al’ummar ƙasar nan wanda duk mai hankali da hangen nesa ya kamata ya ba wa kansa amsa, abin dubawa ne. Domin yadda ‘yan siyasa suke wasan kwaikwayo da ‘Yan Nijeriya ya zama wajibi ne kowa ya san inda ya dosa, sun bari ana ta asarar rayuka ba-ji-ba-gani amma siyasarsu kawai suka sa gaba. Ɗan arewa ya zama Ɗanbora, an ware shi a ƙasar nan bai da wani kataɓus. A kashe shi, a tafi da iyalinsa, a sace dukiyarsa duk babu mai nuna damuwa a cikin waɗannan ‘yan siyasar illa sha’anin gabansu kawai. Waɗanne irin mutane ne muke da su a matsayin shugabanni? Jinin ɗan arewa yana kwarara amma kowa siyasarsa kawai ya sa gaba.

“Duk wani babba da ya ce yana tare da talaka ya zama abin ƙyama a gun ɓata-garin shugabannin Nijeriya, ina jami’an tsaronmu masu kishin Nijeriya? Kuna ina ne ake yi wa ƙannenku da iyayenku kisan gilla babu wani shugaban da ke yin magana? Dan haka muna kira ga matasa da sauran ƙungiyoyin ‘yan arewa da mu nema wa kanmu mafita tun kafin lokaci ya ƙure mana.” In ji shi.

ADVERTISEMENT

Alhaji Ibrahim ya kuma nuna damuwa a kan rashin ‘yanto mutanen da aka sace ana garkuwa da su waɗanda ya ce Allah kaɗai ya san irin azabar da suke sha a hannun ‘yan ta’adda.

Ya ƙara da cewa, “ina mutanen da aka sace a jirgin ƙasan da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna, tambaya a nan ita ce idan kwangila waɗansu suka karɓa don a yi mana wannan kisan mummuƙe a fito fili a yi mana bayani, domin yadda ɗan arewa ya zama a ƙasar nan a yau dabba ta fishi daraja, cin zarafin ya yi yawa mutaƙar gaske. Don haka muna mkira ga ‘Yan Nijeriya musamman ‘yan arewa mu san su waye za mu mara wa baya da za su zama mana tudun tsira a zaɓen 2023, idan ba haka ba, za mu ci gaba da zama jiya-i-yau kuma ba za mu yarda da hakan ba.” Ya bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

 

 

 

Yan Nijeriya
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Na Kasar Sin Kusan Dubu 50 Sun Shiga Ayyukan Kare Zaman Lafiya Na MDD

Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Na Kasar Sin Kusan Dubu 50 Sun Shiga Ayyukan Kare Zaman Lafiya Na MDD

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.