ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Mu Hankalta, Wasan Kwaikwayo ‘Yan Siyasa Ke Yi Da Mu, In Ji Matasan Arewa A Kudu

by yahuzajere
4 years ago
Yan Nijeriya

Shugaban Matasan Arewa A Kudu, Alhaji Ibrahim Ya'u Galadanci

Abubuwan da ke faruwa a ƙasar nan sun nuna ƙarara ‘yan siyasarmu ba komai suke yi ba illa wasan kwaikwayo da rayukan mu ‘Yan Nijeriya, don haka kowa ya san alƙiblar da zai bi. Shugaban Gamayyar Matasan Arewa a Kudancin Nijeriya da ke Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya furta haka domin nuna damuwarsa kan zubar da jini da nakasta ‘yan arewa da ake ci gaba da yi a kullu yaumin.

  • 2023: Duk Sanatocin Bauchi Masu Ci Babu Mai Komawa Sun Sha Kaye A Mazabunsu
  • 2023: Jm’iyyar APC Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugabancin Nijeriya

Ya bayyana haka ne yayin da yake kokawa a wata sanarwa ga manema labarai inda ya yi bayanin cewa, “yadda shugabannin siyasar ƙasarmu Nijeriya suke cutar da al’ummar ƙasar nan wanda duk mai hankali da hangen nesa ya kamata ya ba wa kansa amsa, abin dubawa ne. Domin yadda ‘yan siyasa suke wasan kwaikwayo da ‘Yan Nijeriya ya zama wajibi ne kowa ya san inda ya dosa, sun bari ana ta asarar rayuka ba-ji-ba-gani amma siyasarsu kawai suka sa gaba. Ɗan arewa ya zama Ɗanbora, an ware shi a ƙasar nan bai da wani kataɓus. A kashe shi, a tafi da iyalinsa, a sace dukiyarsa duk babu mai nuna damuwa a cikin waɗannan ‘yan siyasar illa sha’anin gabansu kawai. Waɗanne irin mutane ne muke da su a matsayin shugabanni? Jinin ɗan arewa yana kwarara amma kowa siyasarsa kawai ya sa gaba.

“Duk wani babba da ya ce yana tare da talaka ya zama abin ƙyama a gun ɓata-garin shugabannin Nijeriya, ina jami’an tsaronmu masu kishin Nijeriya? Kuna ina ne ake yi wa ƙannenku da iyayenku kisan gilla babu wani shugaban da ke yin magana? Dan haka muna kira ga matasa da sauran ƙungiyoyin ‘yan arewa da mu nema wa kanmu mafita tun kafin lokaci ya ƙure mana.” In ji shi.

ADVERTISEMENT

Alhaji Ibrahim ya kuma nuna damuwa a kan rashin ‘yanto mutanen da aka sace ana garkuwa da su waɗanda ya ce Allah kaɗai ya san irin azabar da suke sha a hannun ‘yan ta’adda.

Ya ƙara da cewa, “ina mutanen da aka sace a jirgin ƙasan da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna, tambaya a nan ita ce idan kwangila waɗansu suka karɓa don a yi mana wannan kisan mummuƙe a fito fili a yi mana bayani, domin yadda ɗan arewa ya zama a ƙasar nan a yau dabba ta fishi daraja, cin zarafin ya yi yawa mutaƙar gaske. Don haka muna mkira ga ‘Yan Nijeriya musamman ‘yan arewa mu san su waye za mu mara wa baya da za su zama mana tudun tsira a zaɓen 2023, idan ba haka ba, za mu ci gaba da zama jiya-i-yau kuma ba za mu yarda da hakan ba.” Ya bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

 

 

 

Yan Nijeriya
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Na Kasar Sin Kusan Dubu 50 Sun Shiga Ayyukan Kare Zaman Lafiya Na MDD

Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Na Kasar Sin Kusan Dubu 50 Sun Shiga Ayyukan Kare Zaman Lafiya Na MDD

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.