• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 

by Sani Anwar and Sulaiman
23 hours ago
Shettima

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Ibrahim Shettima, ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa; nan ba da jimawa ba, za a kawo karshen matsalar tattalin arzikin da kasar ke fama da shi, a wani sabon mataki na bunkasa tattalin arzikin kasar.

 

Da yake jawabi, a yayin taron sabunta samar da makamashi a Nijeriya (NREIF) ranar Talata a Abuja, Shettima ya ce; zuciyar Shugaba Bola Ahmed Tinubu na tare da ‘yan Nijeriya, sannan kuma yana sane da irin radadin da suke ji.

  • Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
  • Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

“Zuciyar shugaban, na matukar rashin jin dadi, dangane da radadin da ‘yan Nijeriya ke fama da shi, amma kuma muna bayar da tabbacin cewa; ana dab da samun saukin warwarewar al’amuran baki-daya.”

Mun samu labarin cewa, Hukumar Raya Wutar Lantarki ta Karkara (REA), ta shirya taron ne domin neman saka hannun jari, wajen samar da kayayyakin da ake sabuntawa a cikin gida.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

Mataimakin shugaban kasar ya bayyana cewa, taron goron gayyata ne na kafa Nijeriya a matsayin cibiyar samar da makamashi tare da sabuntawa a Afirka, sannan kuma sauyin da aka samu na makamashi Nijeriya, ya bayar da damar zuba jari na sama da dala biliyan 410, daga tsakanin yanzu zuwa shekarar 2060.

Ya kara da cewa, “Daga cikin wannan, ana kuma bukatar sama da Naira biliyan 23, domin fadada hanyoyin samar da makamashin da kuma hada miliyoyin ‘yan Nijeriya, wadanda har yanzu suke rayuwa cikin matsalar wutar lantarki, amma yanzu babban burinmu shi ne, samar da tsarin samar da wutar lantarki mai karfin mega wat 277, nan da shekarar 2060. Cikar wannan buri, ya wuce batun zuba hannun jari kadai, domin yana bukatar kirkire-kirkire, bayar da gudunmawa a cikin gida da kuma sadaukarwa.

“Wannan shi ne dalilin da yasa taken taron na bana ya kasance a matsayin, Aiwatar da Manufofin Nijeriya na Farko da Gudanar da Ci gaban Abubuwan Cikin Gida da kuma Samar da Makamashi, yana da matukar muhimmanci. Kazalika, yunkurinmu na dabarun masana’antu a Nijeriya na kira gare mu da mu dage kan makomar hanyoyin samar da makamashi na Afirka a nan gida.”

Ya kara da cewa, a karkashin wannan, an hada sama da dala miliyan 400 na sabbin alkawuran saka hannun jari a bangaren sabunta makamashi mai a Nijeriya.

“Wannan ya hada da na’urorin hasken rana na sola da fanel-fanel, mita ta zamani, batiri da sauran makamantansu. Babu shakka, ana hasashen wadannan kayayyaki za su samar da ayyukan yi kai tsaye sama da 1,500 a fadin jihohi da dama da kuma nuna kwarin gwiwa a duniya, kan shirin samar da makamashi mai tsafta a Nijeriya”.

A nasa bangaren, Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu ya ce; taron NRIP na 2025, ba wani taro ne da kawai aka shirya ba, sai dan shelanta cewa, Nijeriya a shirye take ta jagoranci sauye-sauyen makamashin da ake samu a Afirka.

Taken taron na bana shi ne, ‘Aiwatar da Manufofin Najeriya na Farko’, yana magana ne a kan wani abu mai mai muhimmanci da ya dara masana’antu, wanda ya kunshi jajircewa, kwarewar masana’antu da kuma dorewar tattalin arziki na tsawon lokaci.

“A bangaren samar da wutar lantarki, manufar Najeriya ta farko ta nuna aniyar tabbatar da cewa; zamani na gaba na fasahar samar da makamashi mai inganci, tun daga na’urori masu amfani da hasken rana har zuwa na’urorin adana makamashin batiri da aka baza a fadin kasar, na alfahari tare da dauke da lakabin, “Wanda aka samar a cikin gida Nijeriya’.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi
Manyan Labarai

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
Next Post
Tinubu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.