• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin ‘Yan Bindiga

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
‘Yan Nijeriya Sun Bukaci Gaggauta Bankado Masu Daukar Nauyin ‘Yan Bindiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon yawaitar ayyukan garkuwa da mutane a cikin Babban Birnin Tarayya Abuja a ‘yan kwanakin nan da ma wasu sassan Nijeriya, lamarin da ya ta da hankalin al’umman kasa da firgitasu.

‘Yan Nijeriyan na kara shiga damuwa a yayin da suke yekuwar a tabbatar da an zakulo ‘yan ta’addan da kuma masu daukan nauyinsu a matsayi wani mataki na kawo karshen matsalolin garkuwa da mutane da neman kudin fansa.

  • Jami’an Tsaro Sun Yi Dirar Mikiya Gidan Dakta Idris Dutsen Tanshi
  • Gwamnatin Zamfara Zata Raba Dabbobi Kyauta Ga Mata

Tsohon dan majalisar dattawa, Sanata Shehu Sani ya shaida a shafinsa na D cewa, za a iya ganowa da samu wadanda suke amfana da makuden kudaden da jama’an kasa ke biya da sunan fansa a duk lokacin da aka sace musu wani nasu.

Ya nuna gayar takaicinsa kan ayyukan ‘yan ta’addan masu garkuwan da mutane da karban miliyoyin daruruwa a hannun jama’a, yayin da kuma suke kunsa musu damuwa da takaici hadi da bakin ciki a duk lokacin da suka sace wani ko wasu.

“Su masu garkuwan mafiya yawansu yara ne wasu ma ‘yan kasa da shekara ashirin. Babu wani alamar morewa ko jin dadi a tattare da su, hatta kayan da suke sanyawa ba za ka ga wani alamin kayan more rayuwa a tattare da su ba, duk kuwa da makuden kudaden da suke amsa a hannun jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

“Tambayar a nan shi ne, su waye ke amfana da makuden kudaden da wadannan masu garkuwa da mutanen ke amsa? Kuma su waye ke samar musu da makamai da suke samun damar gudanar da ayyukan ta’addanci da su?,” Sanatan ya tambaya.

Rahotonni sun zo a baya-bayan da tsohon dan majalisar wakilai, Hon. Sani Muhammad Takori ya yi zargin cewa, ayyukan ‘yan ta’adda a Jihar Zamfara na samun goyon baya daga wasu jiga-jigan mutane.

Kazalika, a baya-bayan nan in za a iya tunawa, gwamnan Jihar Filato, Caleb Muftwang, ya fito balo-balo ya ce, jami’an tsaro sun san wadanda suke amfana da aikace-aikacen ta’addanci a jihar.

Da yake ganawa da wata gidan talabijin, gwamnan wanda ke maida bayani kan hare-haren baya-bayan nan a jihar da ya lakume rayukan mutum sama da 200, ya ce, su ma ‘yan ta’addan an san su.

“Abun da zan iya fada muku kan kashe-kashe da hare-haren Filato a baya-bayan nan tsagwaran ta’addanci ne.

“Na yi imanin masu daukan nauyin ‘yan ta’addan nan da masu cin gajiyar ta’addancin da masu dauke da makaman an sansu. Jami’an tsaro sun sansu, sun san maboyarsu. Wannan dalilin ne ya sa muka nace kan cewa dole ne hukumomin tsaro su yi aikinsu, su tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’umma,” ya shaida.

Wani masanin harkokin tsaro, Mista Akogwu John, ya nuna matukar mamakinsa kan yadda hukumomin tsaro da gwamnatin tarayya suka yi gum kan wannan ikirarin na gwamnan Filato.

Ya ce, “Gwamnan Filato ya fito baro-baro ya ce hukumomin tsaro sun san wadannan mutanen wadanda suke haifar da wannan matsalar a ko’ina. Ban ga labarin yadda hukumomin tsaro suka karyata wannan ikirarin ba. Kenan akwai kamshin gaskiya.

“Muna rayuwa a kasar da komai ana wasu da shi har da lamarin tsaro. Su waye wadannan jiga-jigai mutane masu karfin da ke daukan nauyin kashe-kashen mutanen da ba su ji ba su gani ba kuma me ya sa gwamnati ta yi gum da bakinta?” ya tambaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Arewa Ta Yi Shirin Yi Wa Matsalar Tsaro Taron Dangi

Next Post

Allah Ya Amintar Da Zuciyar Manzon Allah (SAW) Tare Da Tausasawa

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

8 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

11 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

12 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

13 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

15 hours ago
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar
Labarai

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

15 hours ago
Next Post
Allah Ya Amintar Da Zuciyar Manzon Allah (SAW) Tare Da Tausasawa

Allah Ya Amintar Da Zuciyar Manzon Allah (SAW) Tare Da Tausasawa

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.