• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Za Su Sha Wahala Matukar Ba A Biyan Alkalai Albashi – Babban Joji

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
joji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Alkalin-alkalan Nijeriya, Olukayode Ariwoola, ya ce ‘yan Nijeriya za su sha wahala sosai muddin aka kasa biyan alkalai albashi mai kyau da alawus-alawus da sauran hakkokinsu.

Ariwoola ya shaida hakan ne a ranar Litinin yayin jin ba’asin jama’a kan shirin kara albashi da alawus ga ma’aikatan sashin shari’a a Nijeriya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace 130 A Zamfara
  • Sanusi II Ya Bar Ribas, Bayan ‘Labarin LEADERSHIP’ Na Sake Naɗa Shi Sarkin Kano

Jin ba’asin wanda kwamitin majalisar dattawa kan harkokin shari’a da kare hakkin Bil’adama da lamuran shari’a ta shirya.

Ariwoola wanda ya samu wakilcin babban Jojin Jihar Borno, Kashim Zannah, ya ce akwai bukatar karin albashin ga ma’aikatan sashin shari’a domin al’umman kasa ne za a yi wa.

“A lokacin da alkalai suka kasance suna samun hakkokinsu yadda ya dace, tabbas za su ba da himma. Amma idan aka samu akasin haka, to lallai ba za su tsaya su maida hankali wajen kare ra’ayin jama’a ba domin su ma suna cikin yanayi na shan wahala.”

Labarai Masu Nasaba

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Ya misalta halin da alkalai suke ciki a kasar nan da yanayi kawai da suke bi na hakuri da juriya, inda ya nuna cewa akwai bukatar a dauki matakin gaggawa wajen shawo kan hakan.
“Halin da alkalai ke ciki na yanayin rashin lafiya ne. Idan mai ba da lafiya bai da lafiya kun ga ba zai iya kokarin warkar da wani ba.”

Alkalin-alkalan Nijeriya ya jinjina wa kwamitin majalisar dattawan kan shirya taron jin ba’asin, inda ya nuna hakan a matsayin wani mataki da za a iya bi wajen shawo kan matsalolin albashi da alawus din alkalai.

Shi kuma a jawabinsa, ministan shari’a, Lateef Fagbemi, ya ce yunkurin karin albashi ga ma’aikatan sashin shari’a ya kasa cimma nasara a gwamnatin da ta shude.

Ya nuna kwarin gwiwar cewa gwamnatin tarayya a karkashin Bola Tinubu za ta yi abun da ya dace wajen karin albashi ga ma’aikatan sashin shari’a lura da muhimmancinsu a cikin al’umma.

Ministan kudi, Wale Edun, ya jinjina wa majalisar kasa kan amincewa da karin duba bukatar karin albashin. Sai ya yi kira a gaggauta amincewa da kudurin domin amfanun sashin shari’a da kasa baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaShari'asiyasar Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganawar Tsoffin Gwamnonin Zamfara Ta Siyasa Ce Ba Tsaro Ba – Gwamnan Jihar

Next Post

Goron Juma’a

Related

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

24 minutes ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

29 minutes ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

1 hour ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

4 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

6 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

21 hours ago
Next Post
Goro

Goron Juma'a

LABARAI MASU NASABA

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.