• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Za Su Sha Wahala Matukar Ba A Biyan Alkalai Albashi – Babban Joji

byKhalid Idris Doya
1 year ago
joji

Babban Alkalin-alkalan Nijeriya, Olukayode Ariwoola, ya ce ‘yan Nijeriya za su sha wahala sosai muddin aka kasa biyan alkalai albashi mai kyau da alawus-alawus da sauran hakkokinsu.

Ariwoola ya shaida hakan ne a ranar Litinin yayin jin ba’asin jama’a kan shirin kara albashi da alawus ga ma’aikatan sashin shari’a a Nijeriya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace 130 A Zamfara
  • Sanusi II Ya Bar Ribas, Bayan ‘Labarin LEADERSHIP’ Na Sake Naɗa Shi Sarkin Kano

Jin ba’asin wanda kwamitin majalisar dattawa kan harkokin shari’a da kare hakkin Bil’adama da lamuran shari’a ta shirya.

Ariwoola wanda ya samu wakilcin babban Jojin Jihar Borno, Kashim Zannah, ya ce akwai bukatar karin albashin ga ma’aikatan sashin shari’a domin al’umman kasa ne za a yi wa.

“A lokacin da alkalai suka kasance suna samun hakkokinsu yadda ya dace, tabbas za su ba da himma. Amma idan aka samu akasin haka, to lallai ba za su tsaya su maida hankali wajen kare ra’ayin jama’a ba domin su ma suna cikin yanayi na shan wahala.”

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Ya misalta halin da alkalai suke ciki a kasar nan da yanayi kawai da suke bi na hakuri da juriya, inda ya nuna cewa akwai bukatar a dauki matakin gaggawa wajen shawo kan hakan.
“Halin da alkalai ke ciki na yanayin rashin lafiya ne. Idan mai ba da lafiya bai da lafiya kun ga ba zai iya kokarin warkar da wani ba.”

Alkalin-alkalan Nijeriya ya jinjina wa kwamitin majalisar dattawan kan shirya taron jin ba’asin, inda ya nuna hakan a matsayin wani mataki da za a iya bi wajen shawo kan matsalolin albashi da alawus din alkalai.

Shi kuma a jawabinsa, ministan shari’a, Lateef Fagbemi, ya ce yunkurin karin albashi ga ma’aikatan sashin shari’a ya kasa cimma nasara a gwamnatin da ta shude.

Ya nuna kwarin gwiwar cewa gwamnatin tarayya a karkashin Bola Tinubu za ta yi abun da ya dace wajen karin albashi ga ma’aikatan sashin shari’a lura da muhimmancinsu a cikin al’umma.

Ministan kudi, Wale Edun, ya jinjina wa majalisar kasa kan amincewa da karin duba bukatar karin albashin. Sai ya yi kira a gaggauta amincewa da kudurin domin amfanun sashin shari’a da kasa baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Goro

Goron Juma'a

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version