• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Sanda Sun Cafke Jarumin Nollywood Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Al'ajabi
0
‘Yan Sanda Sun Cafke Jarumin Nollywood Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an hukumar  ‘Yan sanda ta Akwa Ibom ta cafke fitaccen jarumin masana’antar shirya fina-finai ta Kudancin Nijeriya ‘Nollywood’, Moses Armstrong, kan zargin yi wa karamar yarinya ‘yar shekara 16 fyade.

Moses Armstrong, tsohon mai taimaka wa gwamnan Jihar Akwa Ibom, Udom Emmanuel a bangaren harkokin noma, ya na tsare ne a sashin kula da manyan laifuka (CID) da ke shalkwatar ‘yan sandan a Ikot Akpanabia.

  • Nijeriya Da Wasu Kasashe Na Asarar Dala Tiriliyan 5 Duk Shekara Saboda Gurbacewar Iska
  • ‘Yan Sanda Sun Ceto Matar Shugaban APC Na Jihar Neja Da Aka Sace A Borno

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa, ofishin matar gwamnan Jihar Akwa Ibom ne ya tsaya kai da fata sai an bi sawun lamarin a karkashin shirinta na taimakon iyali na ‘Family Empowerment and Youth Re-Orientation Path Initiative’ ( FEYReP).

Wani ma’aikacin ofishin matar gwamnan da ya nemi a sakaye sunansa ya shaida ma wakilinmu cewa, “Matar gwamnan ta na da ra’ayi sosai kan wannan kes din domin ganin an yi adalci kan yarinyar da aka keta wa haddi duk kuwa da cewa wanda ake zargin yana aiki a karkashin mijinta a matsayin daya daga cikin hadimansa.

“Ita matar gwamna ta damu sosai kan wannan lamarin, lura da cewa kes ne na fyade kuma kan karamar yarinya, ba ma kawai fyade ga karamar yarinya ba, ta tsani fyade da sauran klamuran da suka shafi cin zarafin mata a cikin al’uma.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

“Don haka a shirye ofishinta ya ke ya bi sawun kes din nan tun daga farko har karshen shari’ar da za a tafka domin hukunta mai laifi da tabbatar da adalci.

“Yanzu haka muna jiran ‘yan sanda ne kawai su kammala gudanar da bincikensu,” a cewar jami’in.

Kazalika, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Supol Odiko Macdon, ya tabbatar da cafke jarumin, “Eh tabbas shi (Armstrong) yana tsare a karkashin kulawarmu, amma a bisa alamu yarinyar da ake magana a kai tana kokarin kaishi kasa ne saboda sun kasance abokai na wasu shekaru.”

A cewarsa Kakakin ‘yan sandan nan kusa kadan za su sake Wanda ake zargin bisa sharadin beli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FyadeKudancin Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Da Wasu Kasashe Na Asarar Dala Tiriliyan 5 Duk Shekara Saboda Gurbacewar Iska

Next Post

Har Yanzu Ilimi Shi Ne Kan Gaba A Gwamnatina – Inuwa Yahaya

Related

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

3 days ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

3 days ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

2 weeks ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi

2 months ago
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
Al'ajabi

Wani Jami’in Ɗansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa

3 months ago
Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja
Al'ajabi

Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja

4 months ago
Next Post
Har Yanzu Ilimi Shi Ne Kan Gaba A Gwamnatina – Inuwa Yahaya

Har Yanzu Ilimi Shi Ne Kan Gaba A Gwamnatina - Inuwa Yahaya

LABARAI MASU NASABA

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.