• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Sanda Sun Cafke Jarumin Nollywood Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Al'ajabi
0
‘Yan Sanda Sun Cafke Jarumin Nollywood Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an hukumar  ‘Yan sanda ta Akwa Ibom ta cafke fitaccen jarumin masana’antar shirya fina-finai ta Kudancin Nijeriya ‘Nollywood’, Moses Armstrong, kan zargin yi wa karamar yarinya ‘yar shekara 16 fyade.

Moses Armstrong, tsohon mai taimaka wa gwamnan Jihar Akwa Ibom, Udom Emmanuel a bangaren harkokin noma, ya na tsare ne a sashin kula da manyan laifuka (CID) da ke shalkwatar ‘yan sandan a Ikot Akpanabia.

  • Nijeriya Da Wasu Kasashe Na Asarar Dala Tiriliyan 5 Duk Shekara Saboda Gurbacewar Iska
  • ‘Yan Sanda Sun Ceto Matar Shugaban APC Na Jihar Neja Da Aka Sace A Borno

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa, ofishin matar gwamnan Jihar Akwa Ibom ne ya tsaya kai da fata sai an bi sawun lamarin a karkashin shirinta na taimakon iyali na ‘Family Empowerment and Youth Re-Orientation Path Initiative’ ( FEYReP).

Wani ma’aikacin ofishin matar gwamnan da ya nemi a sakaye sunansa ya shaida ma wakilinmu cewa, “Matar gwamnan ta na da ra’ayi sosai kan wannan kes din domin ganin an yi adalci kan yarinyar da aka keta wa haddi duk kuwa da cewa wanda ake zargin yana aiki a karkashin mijinta a matsayin daya daga cikin hadimansa.

“Ita matar gwamna ta damu sosai kan wannan lamarin, lura da cewa kes ne na fyade kuma kan karamar yarinya, ba ma kawai fyade ga karamar yarinya ba, ta tsani fyade da sauran klamuran da suka shafi cin zarafin mata a cikin al’uma.

Labarai Masu Nasaba

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

“Don haka a shirye ofishinta ya ke ya bi sawun kes din nan tun daga farko har karshen shari’ar da za a tafka domin hukunta mai laifi da tabbatar da adalci.

“Yanzu haka muna jiran ‘yan sanda ne kawai su kammala gudanar da bincikensu,” a cewar jami’in.

Kazalika, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Supol Odiko Macdon, ya tabbatar da cafke jarumin, “Eh tabbas shi (Armstrong) yana tsare a karkashin kulawarmu, amma a bisa alamu yarinyar da ake magana a kai tana kokarin kaishi kasa ne saboda sun kasance abokai na wasu shekaru.”

A cewarsa Kakakin ‘yan sandan nan kusa kadan za su sake Wanda ake zargin bisa sharadin beli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FyadeKudancin Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Da Wasu Kasashe Na Asarar Dala Tiriliyan 5 Duk Shekara Saboda Gurbacewar Iska

Next Post

Har Yanzu Ilimi Shi Ne Kan Gaba A Gwamnatina – Inuwa Yahaya

Related

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

1 day ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

3 days ago
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

3 months ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

3 months ago
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

4 months ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

5 months ago
Next Post
Har Yanzu Ilimi Shi Ne Kan Gaba A Gwamnatina – Inuwa Yahaya

Har Yanzu Ilimi Shi Ne Kan Gaba A Gwamnatina - Inuwa Yahaya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.