• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Sanda Sun Cafke Jarumin Nollywood Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Al'ajabi
0
‘Yan Sanda Sun Cafke Jarumin Nollywood Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an hukumar  ‘Yan sanda ta Akwa Ibom ta cafke fitaccen jarumin masana’antar shirya fina-finai ta Kudancin Nijeriya ‘Nollywood’, Moses Armstrong, kan zargin yi wa karamar yarinya ‘yar shekara 16 fyade.

Moses Armstrong, tsohon mai taimaka wa gwamnan Jihar Akwa Ibom, Udom Emmanuel a bangaren harkokin noma, ya na tsare ne a sashin kula da manyan laifuka (CID) da ke shalkwatar ‘yan sandan a Ikot Akpanabia.

  • Nijeriya Da Wasu Kasashe Na Asarar Dala Tiriliyan 5 Duk Shekara Saboda Gurbacewar Iska
  • ‘Yan Sanda Sun Ceto Matar Shugaban APC Na Jihar Neja Da Aka Sace A Borno

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa, ofishin matar gwamnan Jihar Akwa Ibom ne ya tsaya kai da fata sai an bi sawun lamarin a karkashin shirinta na taimakon iyali na ‘Family Empowerment and Youth Re-Orientation Path Initiative’ ( FEYReP).

Wani ma’aikacin ofishin matar gwamnan da ya nemi a sakaye sunansa ya shaida ma wakilinmu cewa, “Matar gwamnan ta na da ra’ayi sosai kan wannan kes din domin ganin an yi adalci kan yarinyar da aka keta wa haddi duk kuwa da cewa wanda ake zargin yana aiki a karkashin mijinta a matsayin daya daga cikin hadimansa.

“Ita matar gwamna ta damu sosai kan wannan lamarin, lura da cewa kes ne na fyade kuma kan karamar yarinya, ba ma kawai fyade ga karamar yarinya ba, ta tsani fyade da sauran klamuran da suka shafi cin zarafin mata a cikin al’uma.

Labarai Masu Nasaba

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

“Don haka a shirye ofishinta ya ke ya bi sawun kes din nan tun daga farko har karshen shari’ar da za a tafka domin hukunta mai laifi da tabbatar da adalci.

“Yanzu haka muna jiran ‘yan sanda ne kawai su kammala gudanar da bincikensu,” a cewar jami’in.

Kazalika, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Supol Odiko Macdon, ya tabbatar da cafke jarumin, “Eh tabbas shi (Armstrong) yana tsare a karkashin kulawarmu, amma a bisa alamu yarinyar da ake magana a kai tana kokarin kaishi kasa ne saboda sun kasance abokai na wasu shekaru.”

A cewarsa Kakakin ‘yan sandan nan kusa kadan za su sake Wanda ake zargin bisa sharadin beli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FyadeKudancin Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Da Wasu Kasashe Na Asarar Dala Tiriliyan 5 Duk Shekara Saboda Gurbacewar Iska

Next Post

Har Yanzu Ilimi Shi Ne Kan Gaba A Gwamnatina – Inuwa Yahaya

Related

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

7 days ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

3 weeks ago
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

1 month ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

2 months ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

2 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

3 months ago
Next Post
Har Yanzu Ilimi Shi Ne Kan Gaba A Gwamnatina – Inuwa Yahaya

Har Yanzu Ilimi Shi Ne Kan Gaba A Gwamnatina - Inuwa Yahaya

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.