• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Sanda Sun Cafke Jarumin Nollywood Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade

byKhalid Idris Doya
3 years ago
'Yan

Jami’an hukumar  ‘Yan sanda ta Akwa Ibom ta cafke fitaccen jarumin masana’antar shirya fina-finai ta Kudancin Nijeriya ‘Nollywood’, Moses Armstrong, kan zargin yi wa karamar yarinya ‘yar shekara 16 fyade.

Moses Armstrong, tsohon mai taimaka wa gwamnan Jihar Akwa Ibom, Udom Emmanuel a bangaren harkokin noma, ya na tsare ne a sashin kula da manyan laifuka (CID) da ke shalkwatar ‘yan sandan a Ikot Akpanabia.

  • Nijeriya Da Wasu Kasashe Na Asarar Dala Tiriliyan 5 Duk Shekara Saboda Gurbacewar Iska
  • ‘Yan Sanda Sun Ceto Matar Shugaban APC Na Jihar Neja Da Aka Sace A Borno

Wasu rahotanni sun tabbatar da cewa, ofishin matar gwamnan Jihar Akwa Ibom ne ya tsaya kai da fata sai an bi sawun lamarin a karkashin shirinta na taimakon iyali na ‘Family Empowerment and Youth Re-Orientation Path Initiative’ ( FEYReP).

Wani ma’aikacin ofishin matar gwamnan da ya nemi a sakaye sunansa ya shaida ma wakilinmu cewa, “Matar gwamnan ta na da ra’ayi sosai kan wannan kes din domin ganin an yi adalci kan yarinyar da aka keta wa haddi duk kuwa da cewa wanda ake zargin yana aiki a karkashin mijinta a matsayin daya daga cikin hadimansa.

“Ita matar gwamna ta damu sosai kan wannan lamarin, lura da cewa kes ne na fyade kuma kan karamar yarinya, ba ma kawai fyade ga karamar yarinya ba, ta tsani fyade da sauran klamuran da suka shafi cin zarafin mata a cikin al’uma.

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

“Don haka a shirye ofishinta ya ke ya bi sawun kes din nan tun daga farko har karshen shari’ar da za a tafka domin hukunta mai laifi da tabbatar da adalci.

“Yanzu haka muna jiran ‘yan sanda ne kawai su kammala gudanar da bincikensu,” a cewar jami’in.

Kazalika, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Supol Odiko Macdon, ya tabbatar da cafke jarumin, “Eh tabbas shi (Armstrong) yana tsare a karkashin kulawarmu, amma a bisa alamu yarinyar da ake magana a kai tana kokarin kaishi kasa ne saboda sun kasance abokai na wasu shekaru.”

A cewarsa Kakakin ‘yan sandan nan kusa kadan za su sake Wanda ake zargin bisa sharadin beli.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Next Post
Har Yanzu Ilimi Shi Ne Kan Gaba A Gwamnatina – Inuwa Yahaya

Har Yanzu Ilimi Shi Ne Kan Gaba A Gwamnatina - Inuwa Yahaya

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version