• English
  • Business News
Sunday, June 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

by Abubakar Abba and Sulaiman
12 hours ago
in Wasanni
0
UEFA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Za a iya cewa mabiya harkar wasanni kalilan ne – idan ma akwai – suka yi hasashen kungiyar Paris Saint-Germain za ta lashe gasar zakarun Turai ta Champions League da aka kammala kafin fara ta. PSG ta cinye Inter Milan 5-0 a binrin Munich na Jamus a wasan karshe, wanda masana suka ce shi ne wasan karshe na farko da wata kungiya ɗaya ta fi mamaye wasan a tarihi.

Wannan ne karon farko da PSG ta lashe gasar, kuma ta biyu da ta yi hakan daga kasar Faransa. Kakar ta shekarar 2024 zuwa 2025 ta zo da abubuwa da dama, ciki har da sabon salon buga wasannin rukuni, da kuma kara yawan tawagogin da ke shiga gasar daga 32 zuwa 36.

 

Ousmane Dembélé

Danwasan gaba na Paris Saint-Germain, Ousmane Dembélé, shi ne hukumar kwallon kafa ta Turai Euefa ta zaba a matsayin mafi hazaka a gasar ta Champions League. Demebele ya kai matsayin ne saboda irin taimakon da ya bai wa zakarun na Faransa ta hanyar jefa kwallaye takwas a raga, da kuma bayar da gudummawar cin wasu shida a wasa 15 da ya buga a gasar ta zakarun turai.

Labarai Masu Nasaba

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Sannan shi ne ya fi kowanne danwasa yunkurin cin kwallo a gasar, inda ya kai hari (attempt) sau 64, 23 daga cikinsu akwai munana (on target) 23.

Ya yi nasarar yanka abokan hamayyarsa har sau 62, sannan ya yi bugun kwana 45.

 

Rapinha

Zakakurin danwasan gaba na Barcelona da Brazil, Rapinha, na cikin ‘yanwasan da suka fi bai wa mabiya harkokin wasa mamaki a kakar wasa ta bana baki daya – ba a Champions League ba kawai. Tare da dan wasan kungiyar Borussia Dortmund, Serhou Guirassy, su ne kan gaba a cin mafi yawan kwallaye da 13 kowannensu. Sai dai Rapinha ya zarta shi da yawan bayar da kwallo a zira a raga, inda yake da guda 9, Guirassy ke da 4.

Rapinha mai shekara 28 ya ci ƙwallo tara da ƙafarsa ta hagu, uku da dama, da kuma ɗaya da kansa. Huɗu daga cikin ƙwallayen da ya ci daga wajen yadi na 18 ne.

Wani abu da ya kamata a lura da shi shi ne babu bugun finareti ko ɗaya cikin ƙwallayen da ya ci a wasa 14 da ya buga.

 

Lamine Yamal

Duniya ta fara maganar dan wasa kuma matashin da ya fi birge ‘yankallo ko shakka babu shi ne Lamine Yamal na Barcelona. Dan wasan na Sifaniyan mai shekara 17 ya taka rawar gani cikin wasanni 13 da hya buga wa kungiyar, inda ya kai hare-hare har sau 52. Daga cikinsu akwai munana 25. Yamal ya ci kwallo biyar sannan ya bayar da uku aka zira a raga. Sannan ya yi nasarar yanka abokan hamayya har sau 109 a gasar, wadda ita ce ta biyu da ya buga wa Barcelona.

 

Serhou Guirassy

Shima dan wasa Serhou Guirassy wani danwasan da ya taka rawar gani a kakar da aka kammala shi ne Serhou Guirassy na Burossia Dortmund da kuma Faransa. Danwasan mai shekara 29 ya jefa kwallaye har 13 a raga – iri daya da na Rapinha – sannan ya bayar gudummawa aka ci wasu hudu cikin wasa 14. Cikin kwallayen da ya ci har da uku rigis ya dura wa Barcelona a wasa na biyu na zagayen kusa da na kusa da na karshe.

 

Harry Kane

Danwasan gaba na Bayern Munich kuma kyaftin ɗin Ingila ya ɗora kan abin da ya saba, inda bai gushe ba sai da ya zira kwallaye 11 cikin wasanni 13 da ya buga wa kungiyar, kazalika, Kane mai shekara 31 ya kai hare-hare 49, cikinsu akwai masu hadari 25. Haka nan, ya bayar da kwallo biyu an zira a raga kafin Inter Milan ta yi waje da su daga gasar a zagayen kusa da na karshe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 

Next Post

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

Related

Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila
Wasanni

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

24 hours ago
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
Wasanni

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

2 days ago
De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
Wasanni

De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

3 days ago
Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa
Wasanni

Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa

3 days ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon

4 days ago
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
Wasanni

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

1 week ago
Next Post
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

LABARAI MASU NASABA

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

June 15, 2025
Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

June 15, 2025
Dan Asalin Tudun Loess

Dan Asalin Tudun Loess

June 15, 2025
Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

June 15, 2025
Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

June 15, 2025
Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

June 15, 2025
APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

June 15, 2025
NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

June 15, 2025
Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

June 15, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.