• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanayin Cin Abinci Da Baccin Annabi Muhammadu (SAW)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani and Sulaiman
8 months ago
in Dausayin Musulunci
0
Manzon Allah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu karatu assalamu alaikum wa rahmtullahi ta’ala wa barkatuh. Idan ba a manta ba a makon da ya gabata muna kan darasi ne a game da abubuwa na al’adar rayuwa da yanayin yadda Annabi Muhammadu SAW yake nasa. Za mu ci gaba daga inda muka tsaya inda a yau darasin zai fi mayar da hankali a kan yanayin cin abinci da baccin Annabi SAW.

Sayyidina Aliyu (Karramallahu Wajhahu) yana cewa, duk wanda ya yi bacci har na tsawon Sa’o’i Uku, to ya biya abin da ya wajaba a kanshi. Larabawa da duk masu hikima na daga Malaman falsafa da likitanci, sun tafi a kan cewa, yana da kyau a karanta cin abinci da bacci. Kamar yadda yakan zama zargi ga mutane na kabilu daban-daban a ce “wa ne ya cika cin abinci”. Babu wani da yake alfahari a ce masa ya cika cin abinci.

  • Tashar Samar Da Wutar Lantarkin Nijeriya Ta Sake Lalacewa A Karo Na 11
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Fa’idojin CIIE Na Ci Gaba Da Karuwa

Amma fa duk da haka, ana nufin karanta cin abinci yadda ba zai illata mutum ba. Domin yawaita cin abinci da shaye-shayen kayayyaki, yana nuni da cewa, mutum yana da zari da handama. Allah Ubangiji ya ce “Kulu washrabu wala tusrifu” ku ci abinci ku sha ruwa amma kar ku yi barna (Malamai sun ce duk kiwon lafiya yana cikin wannan ayar).

Yawaita cin abinci yana jawo cutar Duniya da Lahira: cutar Duniya, Ita ce: idan ka kashe Naira N5,000 wurin cin abincin hadama, to akwai yiwuwar kashe ninkin abin da ka kashe wurin cin abincin hadama don neman lafiya, misalin irin su ciwon Siga, Ulcer da dai sauransu. Cutar Lahira, ita ce: Mutum ba zai yi kuzari ba wajen yin Ibada, sabida cututtukan gabobi za su tunkaro masa. Ana cewa, kyawun namiji in ya bi abu (kamar farautar dabbobi) to ya kama abun, amma in shi ne ya tsare ma abun to kar abun ya cimma sa. Haka Larabawa suke gwada namiji.

Akwai wasu mutane da suke gwada hankalin mutum da amfani da tsakuwa: suna zuwa wajen mutum ne yayin da yake bacci sai a jefa masa tsakuwar a gani ko zai farka, in ya farka to ya yi hankali, in bai farka ba to akwai bukatar a sake kula da hankalinsa.

Labarai Masu Nasaba

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Sai dai, galibi masu karanta abinci, za ka same su suna shan kayan itatuwa wanda zai taimaka ma jininsu bugawa. Amma karanta abinci da bacci yana nuni da cewa mutum yana da wadatar zuciya, sabida yakan iya kula da tsarin jikinsa, sannan kuma karanta abinci da bacci yana tumbuke sha’awa. Sakamakon hakan, sai ya kara wa mutum lafiya da karfin tunani da kaifin hankali.
Yawaita bacci, yana nuni da alamar mutum mai kasala ne, yana kawo karancin fahimta da kaifin tunani sannan kuma zai tozarta rayuwarsa a kan bacci da mutuwar zuciya. Wannan karatu ne da kowa ya san shi a al’ada, don haka, ba a bukatar hujjar aya ko hadisi.

Saboda haka, duk wanda ya karanta ko ya yawaita bacci sai an ga wadannan siffofin da muka lissafa. Amma kuma duk da haka, akwai maganganun mutane masu hikima da maganganun al’ummatai daban-daban da wakokin larabawa da hadisan Annabi Muhammad SAW da suke tabbatar da wadannan hikimomin.

Don haka, duk tarihin Annabi SAW za kaji yana karanta bacci da cin abinci. Akwai hadisi da aka ruwaito Annabi SAW ya jera kwanaki Uku yana azumi, “Ba Sahur ba buda baki” Sahabbai za su yi ya ce musu, A’a “ni ina kwana wurin Ubangijina, yana ciyar da ni kuma yana shayar dani”, haka kuma, in ka ji tarihin rayuwar Annabi SAW kan yadda yake bacci, abu ne da hankali ba zai fahimta ba.

An karbo hadisi daga mikdahi, ya ce, Annabi SAW ya ce, “Dan Adam bai cika wata jaka ko kwarya ba, mafi muni irin cikinsa”. Ya ishi dan Adam daga cin abinci na wasu ‘yan lomomi – Na Safe, Rana da dare. In mutum ba zai iya yin ‘yan lomomi ba, to, masu hikima suka ce ya raba cikinsa gida Uku: bangaren Abinci da Ruwa da Numfashi.

Malam Sufyanus Sauri, yana cewa: da karanta abinci ake mallakar bacci a dare, amma in ciki ya cika babu abin da zai rage, sai bacci.

Wasu bangare daga cikin magabata, sun ce, “Kar ku ci abinci da yawa, sai ku yi ta bacci da yawa, sai kuma ku yi asara da yawa (Babu Ibada ballantana Zikiri).

An ruwaito daga Annabi SAW cewa “Mafi soyuwar abinci a wurin Annabi SAW shi ne, wanda aka ci a cikin taro, hannaye suka yi yawa cikin abincin”.

An ruwaito daga Sayyada A’isha Ummil Mu’uminina tana cewa, “cikin Annabi bai taba cika ba da dai,” Manzon Allah SAW ya kasance a cikin Iyalinsa bai tambayar abinci, abin da aka ciyar da shi sai ya karba, haka ma abin da aka shayar da shi sai ya karba”.

Rayuwar Annabi Muhammmad SAW sabanin tamu ce, abin da Allah ya ba shi na hadiyya daga Mutane, sai ya bai wa kowacce daga cikin Matansa, abincin Shekara.

Karanta abinci, kowa da irin zuhudunsa, kar ka matsa wa iyalinka dole sun bi irin zuhudunka.

Ma’ana: Abin da hadisin yake nufi shi ne, Annabi SAW yana baiwa matansa kowacce abincin shekara, sabida haka abincin ya zama nata, ta yi yadda take so da shi, to duk abin da ta yi ta ba shi sai ya karba sabida nata ne shi kuma ba shi aka yi.

Akwai wani hadisi na Barira ‘yar aikin daya daga cikin matan Annabi ce, SAW, wata rana an ba ta sadakar mama, ta sa a wuta tana dafawa, sai Annabi SAW ya zo wucewa sai ya gani ana dafa nama, bayan kai masa abinci sai bai ga an sa masa nama ba (Annabi SAW ya san iyalinsa ba za su samu abu su hana shi ba), sai Matarsa ta ce ya Rasulallahi, Sadaka ce aka bai wa Barira, mu kuma ba ma cin Sadaka, sai Annabi SAW ya mayar mata da amsa cewa, Barira nata Sadaka ce, ni kuma ta ba ni kyauta.

Da irin wannan ne malamai suka yanke hukuncin cewa, in ba ka cin sadaka, sai aka bai wa wani, shi kuma ya kai ma wanda ba ya cin Sadaka, to ya amsa, shi a wurinsa yanzun, kyauta ce.

Yana daga darajar aure, mata ba ta tuhumar mijinta a kan abin da ya ba ta, shi ma baya tuhumar matarshi a kan abin da ta bashi. Sabida dukkansu sun san akwai soyayya da rahama a zuciyarsu. Da wani abin jarrabawa zai taso, da a baya zai sa su sai abin ya fara gamawa da shi tukunna kafin ya isa wurinsu.

Yazo daga cikin hikimomin Lukmanal hakimu: “In ka cika cikinka, sai hankalinka ya yi bacci, ba za ka iya tunani ba, sai gabbai su kasa yin Ibada”
Akwai wani almajirin Imam Malik yana cewa “Ka bar wa Malamai Ilimi in ba za ka karanta cin abinci ba”.

Ya zo a cikin hadisi, Annabi SAW yana cewa, “Ni ba na cin abinci ina kishingide” abin da Malamai suka fassara da shingida a nan shi ne, Zaman dirshan don cin abinci, yana ba wa mai cin abincin damar cin abinci mai yawa, sabida tsari da yanayin zaman yana ba wa mai zaman damar cin abinci sosai.

Manzon Allah SAW yana cewa: “innama ana abdun, a’akulu kama ya’a kulul abdu wa’ajlisu kama yajlisu”, ni bawa ne, ina cin abinci kamar yadda bawa ke ci, kuma ina zama kamar yadda yake zama” a wannan hadisin, yana nufin ba zaman a kishingida ba, a’a zama kamar irin na takama.

Haka baccin Annabi SAW ya kasance kadan ne, kuma a gefen hannun dama yake kwanciya. Bacci a gefen dama ba ya nauyi, ba wuya mutum ya farka, sabida zuciya tana gefen hakarkari na dama, ma’ana a wannan yanayin baccin zuciya tana sama, amma in ka kwanta a bangaren hagu, ka danne ta, don haka bacci zai yi nauyi.

Duk hadisai ingatattu da aka ruwaito sun tabbatar da karanta baccin Annabi SAW. Kuma duk da cewa baccin kadan ne amma sai ga Hadisi yana cewa: “inna ainaiya tanamani, wala yanamu kalbi”, idanuna ce kadai take bacci amma zuciyata ba ta bacci.
Amma mu kuma, mu yi bacci ba mu jin komai, shi ne mun yi bacci. Da yawa za ka ji mai bacci yana cewa masu surutu kusa da kaina duk sun hana ni yin bacci, kuma duk da cewa ya kulle idanuwansa, amma SAW ya ce shi hakan shi ne baccinshi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Barhama InyasManzon Allah SAW
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Zai Halarci Taron APEC Da Na G20, Tare Da Ziyarar Aiki A Peru Da Brazil

Next Post

IPMAN Ta Bayyana Dalilin Rashin Fara Sayen Man Fetur Daga Matatar Dangote

Related

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

5 hours ago
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

1 week ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)
Dausayin Musulunci

Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)

2 weeks ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

3 weeks ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

1 month ago
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci
Dausayin Musulunci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

1 month ago
Next Post
Matatar dangote

IPMAN Ta Bayyana Dalilin Rashin Fara Sayen Man Fetur Daga Matatar Dangote

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

June 27, 2025
Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

June 27, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.