ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IPMAN Ta Bayyana Dalilin Rashin Fara Sayen Man Fetur Daga Matatar Dangote

by Bello Hamza and Sulaiman
2 years ago
Matatar dangote

Biyo bayan sabuwar takaddama na sayen tataccen mai daga matatar Dangote, kungiyar dillan mai ta kasa IPMAN, ta sanar da cewa, ta na kan tattaunawa da matatar Dangote, dangane da fara sayen mai, daga matatar ta Dangote.

Shugaban rukunin matatar man Dangote Alhaji Aliko Dangote, ya yi zargin cewa, kamfanin kula da albarkatun main a kasa NNPCL, tare da sauran masu ruwa da tsaki, suna shigo da man daga wasu kasashen duniya, suna kuma kin sayen wanda matatarsa ke tacewa.

  • Karin Kayayyaki Daga Kasashe Mafi Karancin Ci Gaba Sun Shiga Kasuwar Kasar Sin Ta Bikin CIIE
  • Zargin Cin Zarafin Likita: Gwamna Yusuf Ya Roki Likitoci Su Bayar Da Kofar Sulhu

Dangote ya kara da cewa, matatarsa, na da karfin da za ta iya samar da tataccen man lita miliyan 500.

ADVERTISEMENT

Sai dai, a martanin da mai magana da yawun IPMAN na kasa Cif Chinedu Ukadike, ya bayyana cewa, kungiyar ba ta riga ta sayo man daga matatar Dangote ba, domin har yanzu, ana ci gaba da tattaunawa a kan batun.

A cewarsa Chinedu,“Har yanzu, bamu karbi kayan daga matatar man ta Dangote ba, amma ana ci gaba da tattaunawa za mu nkuma sanar idan mun fara karbar kayan daga matatar.”

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

A daya bangaren Chinedu ya bayyana cewa, karin farashin mai da kamfanin NNPCL bayan kwanuka biyu, ba abin mamaki bane duba da yadda kasuwar ta kasance.

Sai dai, duk da karin Naira 30 na kowacce Litar mai daya, wanda ya kai kaso 3 a cikin dari zuwa Naira 1, 060 na kowacce lita daya a Abuja, dilallan man sun ci gaba da sayar da man a watan Okotobar 2024 a kan farasahin da take sayarwa.

Wani bincike da Jaridar Banguard ta gudanar ya nuna cewa, manyan dillalan man kamar su, Conoil and TotalEnergies, sun ci gaba da sayar da man su a kan farashin Naira 1,109, NIPCO akan farshin Naira N1,115, Adoba Plc a kan Naira N1,125, inda kuma akasarin dilalan man, ke sayar da man a kan Naira 1,150 – N1,230.

A kwannan baya ne NNPC ya kara farashin wanda ya kai kashi 14.8 a ranar 9 ga watan Okotobar, 2024, inda karin farashin man ya kai daga Naira 897 zuwa Naira to 1, 030 na kowacce lita daya, bayan cire tallafin mai da gwamnatin tarayya ta yi.

Wannan karin ya sabawa tunanin yarjejiya a tsakanin gwamnatin tarayya da matatar man Dangote, na sayar da danyen mai a farashin Naira mai makon da farashin dala wanda hakan ya sanya farashin ya fara raguwa a ranar 1 ga watan Oktobar 2024.

Karin na kwanan nan, da aka yi a ranar 3 ga watan Satumbar 2024 ya faru ne, bayan NNPC, ya kara farashin litar man zuwa kashi 45, inda farashin ya karu daga Naira 617 zuwa Naira to 897 na kowacce litar man daya.

IPMAN
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja
IPMAN
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tattalin Arziki

Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas

May 24, 2026
Next Post
Noma

Harajin "VAT" Zai Kara Wa Al'ummar Kasar Nan Kuncin Rayuwa Ne Kawai - Gambo Danpass

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.