• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan Jihar Katsina, DSP Abubakar Sadik, ya ce rundunar ta fara gudanar da bincike kan wani harbin da wani jami’in ‘Cibilian Joint Task Force’ ya yi wanda ya yi sanadin mutuwar dalibin jami’ar tarayya mai matakin karatu na 400 da ke Dutsinma a jihar domin cafke wanda ya aikata laifin.

Sadik ya bayyana haka ne a wata sanarwa da ya fitar a Katsina.

  • Japan Ta Kirkiro Da Sabuwar Kimiyyar Samar Da Ingantacciyar Madarar Shanu
  • Kwastam Da Hukumar NPA Sun Kulla Hadakar Bunkasa Ingancin Aiki A Tashoshin Jiragen Ruwa

A cewar sanarwar, “Rundunar ‘yansandan Jihar Katsina ta fara gudanar da bincike kan wani harbin da wani jami’in rundunar hadin gwiwa na Cibilian Task Force ya yi. Lamarin ya yi sanadiyar raunata wani direban okada da kuma mutuwar wani dalibi mai mataki 400 na jami’ar tarayya ta Dutsinma.

“Rahotanni na farko sun nuna cewa, a ranar 23 ga Fabrairu, 2025, da misalin karfe 11:26 na safe, wani direban babur na haya da ke jigilar fasinja, Sa’idu Abdulkadir, ya hadu da tawagar CJTF a cikin motar Hilud. Daya daga cikin ‘yan JTF din ya yi harbin kan wadanda lamarin ya rutsa da su, lamarin da ya yi sanadin jikkatar mai babur din.

“Ba tare da bata lokaci ba jami’an ‘yansanda suka kai dauki inda suka garzaya da wadanda abin ya shafa zuwa babban asibitin Dutsinma. Daga baya aka mika Sa’idu asibitin kashi na Katsina, inda aka tabbatar da cewa ya rasu da isarsa.”

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Ya bayyana cewa rundunar ta damu matuka da faruwar lamarin, kuma ta himmatu wajen tabbatar da an yi adalci, yana mai cewa “Muna hada kai da hukumomin makarantar da sauran masu ruwa da tsaki domin zakulo wadanda ake zargin tare da kama su.

Za a sanar da ci gaban lamarin a kan lokaci,” in ji shi.

Tun da farko dai, jaridar PUNCH Metro ta ruwaito cewa, a ranar Litinin din da ta gabata ne mahukuntan jami’ar suka rufe makarantar, sakamakon zanga-zangar da dalibai suka yi kan kisan abokin aikinsu.

Wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta, ta shaida wa wakilinmu a Katsina a safiyar ranar Litinin cewa, “wasu jami’an CJTF sun bindige dalibai biyu ne bisa kuskure, suna tunanin ‘yan fashi ne.

“Daya daga cikin daliban ya mutu nan take yayin da daya kuma aka harbe shi a kafa, kuma tuni aka kai shi asibiti domin kula da lafiyarsa.

“Bayan wannan ci gaba, dalibai sun shiga zanga-zanga tun jiya lokacin da lamarin ya faru, inda suka fito kan tituna a Dutsinma, suna kona motoci tare da lalata dukiyoyi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaKatsina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Kwana 22, Tsohon Shugaban NYSC Tsiga Ya Kuɓuta A Hannun Ƴan Bindiga

Next Post

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

4 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Uku Da Kokon Kan Mutum A Imo

3 months ago
Next Post
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.