• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

by Rabi'u Ali Indabawa
2 hours ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Kebbi ta kama wasu mutum hudu da ake zargi da lalata wata na’urar taransifoma a makarantar sakandiren mata ta gwamnati da ke Bunza a Karamar Hukumar Bunza a jihar.

Wadanda ake zargin sun hada da Sanusi Muhammad da Ibrahim Lawal daga Jihar Sokoto da Tasi’u Abubakar da Tasi’u Abdullahi daga Jihar Zamfara, an kama su ne bayan da jami’in ‘yansanda reshen Bunza da tawagar ‘yan banga suka kai daukin gaggawa.

  • Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Kakakin rundunar ‘yansandan, CSP Nafiu Abubakar, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, ya ce wadanda ake zargin sun cika harabar makarantar ne da misalin karfe 3 na dare, inda suka daure mai gadin makarantar kafin daga bisani suka fasa na’urar taranfoma dake daure da sarkoki da sauran kayan aikin injiniya.

Ya ce, “An gano wata bakar mota kirar Toyota Corolla mai lamba KNT-359-SN, wacce ake kyautata zaton wadanda ake zargin sun yi amfani da ita, a wajen da lamarin ya faru, tare da barnata wayoyi masu sulke da kuma kayan aikin da aka yi amfani da su wajen aikata laifin.

“Yayin da aka kama biyu daga cikin wadanda ake zargin nan take, wani bincike mai zurfi da hukumar binciken manyan laifuka ta jihar (SCID) ta gudanar a Birnin Kebbi, ya kai ga kama ‘yan kungiyar da suka gudu.”

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Ya kara da cewa wadanda ake zargin suna nan a gidan yari kuma nan ba da jimawa ba za a gurfanar da su a gaban kotu domin hukunci.

Kwamishinan ’Yansandan Jihar, CP Bello M. Sani, ya yaba wa kwazon da DPO da ’yan banga suka yi da gaggawa, inda ya jaddada muhimmancin hadin kan ‘yansanda da al’umma wajen magance miyagun laifuka.

Ya kuma tabbatar wa mazauna Jihar Kebbi cewa, rundunar ‘yansandan ta jajirce wajen kawar da masu aikata laifuka da samar da yanayi mai tsaro. Daga nan sai ya bukaci jama’a da su sanya ido tare da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin daukar matakin gaggawa.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, rundunar ‘yansandan Jihar Kebbi ta kama wasu mutane shida da ake zargi da satar kayan ado na zinare da suka kai sama da Naira miliyan 109.5 a garin Ka’oje da ke Karamar Hukumar Bagudo.

Al’amarin ya dauki hankula sosai bayan kama Ibrahim Abubakar, jami’in hukumar gidan gyaran hali ta Nijeriya, wanda ya amsa laifinsa. Kayayyakin da aka sace na iyalan Hajiya Amina Hassan Bello, sun hada da sarkar gwal guda biyar, bangulu guda tara, da zobe hudu masu nauyin gram 782.7.

A cewar rundunar ‘yansandan, dansandan ya hada baki ne da ‘yan fashin wajen sayar da gwal din da aka sace tare da karkatar da kudaden ta hanyar mallakar filaye. Ana ci gaba da gudanar da bincike don zakulo wasu da ake zargi da kuma kwato wasu kadarori.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

Next Post

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

49 minutes ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

1 month ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

1 month ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

1 month ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

1 month ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

1 month ago
Next Post
Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

September 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

September 27, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

September 27, 2025
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

September 27, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.