• English
  • Business News
Thursday, October 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kama Ɓarayi A Jihar Neja

by Sadiq
3 hours ago
in Manyan Labarai
0
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘Yansandan Jihar Neja, ta kashe masu garkuwa da mutane uku a wani samame da ta kai dajin Kokolo, Nasko a ƙaramar hukumar Magama, a ranar 12 ga watan Satumba, 2025.

Kakakin rundunar, Wasiu Abiodun, ya bayyana cewa jami’an ‘yansanda sun yi musayar wuta da masu garkuwar kafin a kashe su.

  • PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai
  • Masana’antar AI Ta Kasar Sin Ta Samu Habaka Da Kamfanoni Fiye Da 5300

Sun ceto mutum ɗaya da aka sace, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga.

An kuma samu bindigogi ƙirar AK-74 guda biyu da harsashi 49 daga maɓoyarsu.

Abiodun ya buƙaci al’umma da su kai rahoton duk wanda suka gani da raunukan harbin bindiga.

Labarai Masu Nasaba

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

A wani samame daban a ranar 25 ga watan Satumba, sashen Anti-Thuggery Unit ya kai farmaki maɓoyar masu laifi a Sabon-Titi, Tunga, Minna, inda aka kama wasu ɓarayi biyu.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Murtala Abbas mai shekaru 18 daga Katsina da kuma Hassan Ibrahim mai shekaru 20 daga Tunga.

An kama su da makamai irin su adduna, bindigogi ƙirar gida, rigar ‘yansanda da miyagun ƙwayoyi.

Hassan ya amsa cewa wani ɗan sa-kai mai suna “Sadiq” ne ya ba shi bindiga da kuma na’urar sadarwa wacce ba ta aiki.

Dukkaninsu suna hannun ‘yansanda a yanzu.

Haka kuma, a ranar 27 ga watan Satumba, ‘yansanda sun kama Bashir Abubakar mai shekaru 28 daga Jihar Kebbi a kasuwar Kontagora bisa zargin zamba.

An ce ya yi ƙoƙarin musanya jakar da ke cike da takardun da ba su da amfani da wayoyi da kayan haɗa da suka kai Naira dubu dari biyar (₦500,000).

An kuma danganta shi da wata zamba a watan Agusta, inda aka sace wayoyin Naira dubu 240 da kuma babur.

Mutane sun kusa yi masa dukan kawo wuƙa kafin jami’an ‘yansanda su ceci rayuwarsa.

An tabbatar da cewa za a gurfanar da shi a kotu bayan kammala bincike.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Neja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

Next Post

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

Related

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus
Manyan Labarai

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

3 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

4 hours ago
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Gargaɗi Kan Yiwuwar Aukuwar Ambaliya A Wasu Jihohi

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP, Sun Kama Wasu Da Miyagun Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP, Sun Kama Wasu Da Miyagun Ƙwayoyi

17 hours ago
Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

21 hours ago
NAPTIP Ta Kama Mutum 5 Da Ake Zargi Da Safarar Mutane A Filin Jirgin Saman Abuja, Ta Ceto Mutane 24
Manyan Labarai

NAPTIP Ta Kama Mutum 5 Da Ake Zargi Da Safarar Mutane A Filin Jirgin Saman Abuja, Ta Ceto Mutane 24

22 hours ago
Next Post
Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta  Barazana Ce Ga Makomar Nijeriya – Obasanjo

October 2, 2025
Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar UNGA Da Jamus

October 2, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kama Ɓarayi A Jihar Neja

October 2, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

October 2, 2025
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Gargaɗi Kan Yiwuwar Aukuwar Ambaliya A Wasu Jihohi

October 2, 2025
Collins Daga BUK Na Dab Da Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

Collins Daga BUK Na Dab Da Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

October 2, 2025
PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

October 1, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP, Sun Kama Wasu Da Miyagun Ƙwayoyi

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP, Sun Kama Wasu Da Miyagun Ƙwayoyi

October 1, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Gwamnatin Amurka Ta Tsayar Da Ayyukanta

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Gwamnatin Amurka Ta Tsayar Da Ayyukanta

October 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.