• English
  • Business News
Wednesday, June 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu nasarar tarwatsawa da wargaza wuraren haɗawa da rabar da taki na bogi guda uku a jihar Bauchi tare da kamo kayayyakin da ake amfani da su wajen haɗa takin na bogi. 

 

A wata sanarwar da kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya fitar a ranar Laraba, ya ce, sun yi amfani da wani rahoton sirri da suka samu a ranar 10 ga watan Mayu wajen kai samamen.

  • Sin Ta Fitar Da Fim Dake Bayyana Al’amaru Na Gaske Bisa Taken “Gajimare A Doron Kasa” 
  • Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

Jami’an sintiri na rundunar sun kai ga kama wani mutum Muhammad Abubakar a gidansa da ke Magaji Quarters Bauchi ɗauke da buhun taki na bogi da aka sarrafa guda 6 da kwalaben maganin ciyawa guda 46.

Jabun taki

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ceto Nijeriya Daga Faɗawa Matsin Tattalin Arziƙi – Gwamna Namadi

Kotu Ta Yi Watsi Da Buƙatun Akpabio Kan Dakatar Da Sanata Natasha

A wani bincike da aka gudanar a gidansa da ke unguwar Magaji Quarters, an gano katan 38 da babu kowa a ciki na maganin ciyawa iri-iri, buhunan NPK guda 14, buhunan Indorama guda 9, jerikan cokali guda biyar, murhun gawayi, daurin ledoji, da buhunan da ke ɗauke da Ztars da garin lambda.

 

Yayin da ake masa tambayoyi, Abubakar ya yi iƙirarin cewa makwancinsa, Abubakar Umar, shi ma na da hannu a lamarin.

 

A ranar 14 ga watan Mayu, bayan wani rahoto na daban, ‘yan sanda sun kai samame a wani shago da ke kan titin Gombe a cikin garin na Bauchi mallakin wani Anas Abubakar mai shekaru 32. An same shi da buhunan 44.5 na gurɓataccen taki

 

Da ya ke fuskantar tambayoyi, Anas ya amsa cewa na samun kayan kaolin da yake amfani da shi wajen haɗa gurɓataccen taki daga wajen wani mai suna Abdulrahaman Muhammad, ɗan shekara 24 mazaunin unguwar Bakaro.

 

Kazalika, jami’an ‘yansandan sun cigaba da zurfafa bincike inda hakan ya kai su ga kamo wani mai suna Ziya’u Bala, ɗan shekara 27 a duniya mazaunin unguwar Gudum Hausawa, wanda ya yi rakiya wa jami’an zuwa wanin wurin da ake aikin haɗa taki ba bisa ƙa’ida a rugar Natsira da ke ƙauyen Kangere. Wurin mai ɗauke da buhu kusan 100 na gurɓataccen taki.

 

‘Yansandan sun kamo buhun jabun taki guda 44, buhun kaolin guda 100, buhun taki 12, da buhun taki urea.

 

Wuraren hada jabun takin guda biyu da Sama’ila Abdullahi, da Mujahid Abdullahi suke gudanarwa a Natsira da Kangere duk an gano su.

 

Duk wanda ake zargi sun ce suna haɗa takin ne tare da sayar ma wani Abdulrahaman, inda shi kuma yake kaiwa ga Anas.

 

Dukkanin wuraren hada takin na jabu guda uku an tarwatsa da kamo kayayyakin da suke amfani da su wajen haɗa gurɓatattun taki.

 

Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi CP Sani-Omolori Aliyu, ya tabbatar da aniyar rundunar na gudanar da masu irin wannan aika-aikar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Next Post

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Related

Tinubu Ya Ceto Nijeriya Daga Faɗawa Matsin Tattalin Arziƙi – Gwamna Namadi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ceto Nijeriya Daga Faɗawa Matsin Tattalin Arziƙi – Gwamna Namadi

1 hour ago
Kotu Ta Yi Watsi Da Buƙatun Akpabio Kan Dakatar Da Sanata Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Buƙatun Akpabio Kan Dakatar Da Sanata Natasha

2 hours ago
Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar
Labarai

Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar

11 hours ago
Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa
Manyan Labarai

Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa

14 hours ago
Mutum 10 Sun Mutu Sakamakon Harbe-harbe A Makarantar Sakandire A Kasar Austriya
Manyan Labarai

Mutum 10 Sun Mutu Sakamakon Harbe-harbe A Makarantar Sakandire A Kasar Austriya

16 hours ago
Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
Ra'ayi Riga

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

17 hours ago
Next Post
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Ceto Nijeriya Daga Faɗawa Matsin Tattalin Arziƙi – Gwamna Namadi

Tinubu Ya Ceto Nijeriya Daga Faɗawa Matsin Tattalin Arziƙi – Gwamna Namadi

June 11, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Buƙatun Akpabio Kan Dakatar Da Sanata Natasha

Kotu Ta Yi Watsi Da Buƙatun Akpabio Kan Dakatar Da Sanata Natasha

June 11, 2025
Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD

Wang Yi Ya Gabatar Da Jawabi Albarkacin “Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa” Karo Na Farko Na MDD

June 10, 2025
Sin Da Kenya Sun Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Kiwon Lafiya

Sin Da Kenya Sun Zurfafa Hadin Gwiwa A Bangaren Kiwon Lafiya

June 10, 2025
Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar

Rashin Tsaro: Gwamnatin Kogi Ta Gargadi Siyasantar Da Kalubalen Tsaro A Jihar

June 10, 2025
Xi Ya Zanta Da Takwaransa Na Kasar Koriya Ta Kudu  

Xi Ya Zanta Da Takwaransa Na Kasar Koriya Ta Kudu  

June 10, 2025
Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu

Kyakkyawar Hulda Tsakanin Sin Da Koriya Ta Kudu Na Da Muhimmanci Ga Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankinsu

June 10, 2025
Sin Na Maraba Da Karin ‘Yan Kasuwar Ketare Dake Son Gudanar Da Hada-hada Don Cimma Moriyar Juna

Sin Na Maraba Da Karin ‘Yan Kasuwar Ketare Dake Son Gudanar Da Hada-hada Don Cimma Moriyar Juna

June 10, 2025
Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa

Gwamna Zulum Ya Bayar Da Tallafin Miliyan 300 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Mokwa

June 10, 2025
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Babban Taron MDD Kan Tekuna

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Babban Taron MDD Kan Tekuna

June 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.