• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta samu nasarar tarwatsawa da wargaza wuraren haɗawa da rabar da taki na bogi guda uku a jihar Bauchi tare da kamo kayayyakin da ake amfani da su wajen haɗa takin na bogi. 

 

A wata sanarwar da kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya fitar a ranar Laraba, ya ce, sun yi amfani da wani rahoton sirri da suka samu a ranar 10 ga watan Mayu wajen kai samamen.

  • Sin Ta Fitar Da Fim Dake Bayyana Al’amaru Na Gaske Bisa Taken “Gajimare A Doron Kasa” 
  • Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

Jami’an sintiri na rundunar sun kai ga kama wani mutum Muhammad Abubakar a gidansa da ke Magaji Quarters Bauchi ɗauke da buhun taki na bogi da aka sarrafa guda 6 da kwalaben maganin ciyawa guda 46.

Jabun taki

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

A wani bincike da aka gudanar a gidansa da ke unguwar Magaji Quarters, an gano katan 38 da babu kowa a ciki na maganin ciyawa iri-iri, buhunan NPK guda 14, buhunan Indorama guda 9, jerikan cokali guda biyar, murhun gawayi, daurin ledoji, da buhunan da ke ɗauke da Ztars da garin lambda.

 

Yayin da ake masa tambayoyi, Abubakar ya yi iƙirarin cewa makwancinsa, Abubakar Umar, shi ma na da hannu a lamarin.

 

A ranar 14 ga watan Mayu, bayan wani rahoto na daban, ‘yan sanda sun kai samame a wani shago da ke kan titin Gombe a cikin garin na Bauchi mallakin wani Anas Abubakar mai shekaru 32. An same shi da buhunan 44.5 na gurɓataccen taki

 

Da ya ke fuskantar tambayoyi, Anas ya amsa cewa na samun kayan kaolin da yake amfani da shi wajen haɗa gurɓataccen taki daga wajen wani mai suna Abdulrahaman Muhammad, ɗan shekara 24 mazaunin unguwar Bakaro.

 

Kazalika, jami’an ‘yansandan sun cigaba da zurfafa bincike inda hakan ya kai su ga kamo wani mai suna Ziya’u Bala, ɗan shekara 27 a duniya mazaunin unguwar Gudum Hausawa, wanda ya yi rakiya wa jami’an zuwa wanin wurin da ake aikin haɗa taki ba bisa ƙa’ida a rugar Natsira da ke ƙauyen Kangere. Wurin mai ɗauke da buhu kusan 100 na gurɓataccen taki.

 

‘Yansandan sun kamo buhun jabun taki guda 44, buhun kaolin guda 100, buhun taki 12, da buhun taki urea.

 

Wuraren hada jabun takin guda biyu da Sama’ila Abdullahi, da Mujahid Abdullahi suke gudanarwa a Natsira da Kangere duk an gano su.

 

Duk wanda ake zargi sun ce suna haɗa takin ne tare da sayar ma wani Abdulrahaman, inda shi kuma yake kaiwa ga Anas.

 

Dukkanin wuraren hada takin na jabu guda uku an tarwatsa da kamo kayayyakin da suke amfani da su wajen haɗa gurɓatattun taki.

 

Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi CP Sani-Omolori Aliyu, ya tabbatar da aniyar rundunar na gudanar da masu irin wannan aika-aikar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Next Post

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

1 hour ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

3 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

5 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

8 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

10 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

11 hours ago
Next Post
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.