• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: An Hana Mataimakin Gwamnan Edo Shiga Ofishinsa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Yanzu-yanzu: An Hana Mataimakin Gwamnan Edo Shiga Ofishinsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarin da muke samu yanzu-yanzu na nuna cewa an hana mataimakin Gwamnan jihar Edo, Comrade Philip Shaibu, shiga ofishinsa da ke Dennis Osadebey Avenue, wato fadar gwamnatin jihar da ke birnin Benin, babban birnin Jihar Edo.

Wannan wani abu ne da ke nuna yadda dangantaka ta ƙara tsami a tsakanin Gwamnan Jihar Edo Andrew Obaseki da mataimakin nasa, Shaibu.

Shaibu wanda ya tafi ofis da niyyar shiga domin gudanar da ayyuka kwatsam sai ya tarar da an kulle kofar shiga.

  • Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango

 

Mataimakin gwamnan da hadimansa sun shafe tsawon awa guda suna tunanin ko daga baya za a bude musu kofar ofishin amma hakan ya ci tura daga bisani dole suka juya.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Shaibu ya yi ta kiran Gwamnan jihar Andrew Obaseki a wayar salula amma bai samu damar magana da shu ba.

Majiyoyi sun shaida cewar Shaibu ya yi magana da kwamishinan ‘yansandan jihar da daraktan ‘yansandan ciki na (DSS) inda ya shaida musu yadda aka kulle masa ofis da hanasa shiga.

Mataimakin Gwamnan ya kira kwamandan tsaron gidan gwamnatin jihar SP Ibrahim Babatunde, inda ya tambaye shi da dalili hana shi shiga ofishinsa, sai ya amsa da cewa umarni ne daga sama. Ya kara da cewa babban jami’in tsaron Gwamna (CSO) Wabba Williams, shi ne ya fi kamata a nemo domin ya yi bayanin da ya dace.

Shaibu ya kira Williams inda ya yi alkawarin cewa yana zuwa amma har tsawon lokacin da mataimakin gwamnan ya shafe yana jira bai zo ba.

“Har zuwa yanzu, ban samu wata sanarwa a hukumance kan inda zan koma ba. Illa wadanda suke da bayanin su ne ma’aikatana. Ma’aikatan gwamnati na da bayanin a hukumance amma ni ba ni da shi. A daidai lokacin nan da nake magana da kai, ina tsaye a mashigar gidan gwamnatin,” Shaibu ya shaida a lokacin da aka jiyo shi yana waya da wani mutum da ba a gane waye ba.

A makon jiya, an ce  a wata wasika daga ofishin shugaban ma’aikatan jihar, Anthony Okungbowa, da aka aike ga babban sakataren ofishin mataimakin Gwamnan, ta unarci Shaibu da ya koma sabon ofishinsa da ke lamba 7 Dennis Osadebey Avenue, GRA, a birnin Benin babban fadar jihar.

LEADERSHIP ta labarto cewa makonni biyu da suka gabata an hango alamin ofishin mataimakin gwamnan a wani sabon ofishi da ake son ya koma da ke da tazarar mitoci da fadar gwamnatin jihar, sai dai Shaibu ya nace kan cewa ba a sanar da shi cewa za a canza masa ofishi da fitar da shi daga fadar gwamnatin ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BeninEdoMataimakin GwamnaShaibu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Kai Wa ‘Yan Bindiga Bayanan Sirri Sun Fi Cutarwa Fiye Da ‘Yan Bindiga – Bala Kaura

Next Post

Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

3 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

5 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

6 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

6 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

10 hours ago
Next Post
Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.