• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: An Hana Mataimakin Gwamnan Edo Shiga Ofishinsa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
hana

Labarin da muke samu yanzu-yanzu na nuna cewa an hana mataimakin Gwamnan jihar Edo, Comrade Philip Shaibu, shiga ofishinsa da ke Dennis Osadebey Avenue, wato fadar gwamnatin jihar da ke birnin Benin, babban birnin Jihar Edo.

Wannan wani abu ne da ke nuna yadda dangantaka ta ƙara tsami a tsakanin Gwamnan Jihar Edo Andrew Obaseki da mataimakin nasa, Shaibu.

Shaibu wanda ya tafi ofis da niyyar shiga domin gudanar da ayyuka kwatsam sai ya tarar da an kulle kofar shiga.

  • Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango

 

Mataimakin gwamnan da hadimansa sun shafe tsawon awa guda suna tunanin ko daga baya za a bude musu kofar ofishin amma hakan ya ci tura daga bisani dole suka juya.

LABARAI MASU NASABA

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

Shaibu ya yi ta kiran Gwamnan jihar Andrew Obaseki a wayar salula amma bai samu damar magana da shu ba.

Majiyoyi sun shaida cewar Shaibu ya yi magana da kwamishinan ‘yansandan jihar da daraktan ‘yansandan ciki na (DSS) inda ya shaida musu yadda aka kulle masa ofis da hanasa shiga.

Mataimakin Gwamnan ya kira kwamandan tsaron gidan gwamnatin jihar SP Ibrahim Babatunde, inda ya tambaye shi da dalili hana shi shiga ofishinsa, sai ya amsa da cewa umarni ne daga sama. Ya kara da cewa babban jami’in tsaron Gwamna (CSO) Wabba Williams, shi ne ya fi kamata a nemo domin ya yi bayanin da ya dace.

Shaibu ya kira Williams inda ya yi alkawarin cewa yana zuwa amma har tsawon lokacin da mataimakin gwamnan ya shafe yana jira bai zo ba.

“Har zuwa yanzu, ban samu wata sanarwa a hukumance kan inda zan koma ba. Illa wadanda suke da bayanin su ne ma’aikatana. Ma’aikatan gwamnati na da bayanin a hukumance amma ni ba ni da shi. A daidai lokacin nan da nake magana da kai, ina tsaye a mashigar gidan gwamnatin,” Shaibu ya shaida a lokacin da aka jiyo shi yana waya da wani mutum da ba a gane waye ba.

A makon jiya, an ce  a wata wasika daga ofishin shugaban ma’aikatan jihar, Anthony Okungbowa, da aka aike ga babban sakataren ofishin mataimakin Gwamnan, ta unarci Shaibu da ya koma sabon ofishinsa da ke lamba 7 Dennis Osadebey Avenue, GRA, a birnin Benin babban fadar jihar.

LEADERSHIP ta labarto cewa makonni biyu da suka gabata an hango alamin ofishin mataimakin gwamnan a wani sabon ofishi da ake son ya koma da ke da tazarar mitoci da fadar gwamnatin jihar, sai dai Shaibu ya nace kan cewa ba a sanar da shi cewa za a canza masa ofishi da fitar da shi daga fadar gwamnatin ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Manyan Labarai

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
Next Post
Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.