Gwamnan jihar Neja, Umaru Bago, ya bayar da umarnin gudanar da bukukuwan karamar Sallah saffa-saffa tare da dakatar da Hawan Bariki, Hawan Sallah da sauran bukukuwan Sallah a dukkan masarautun jihar.
Umurnin ya biyo bayan mummunan bala’in ambaliya da ta yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyi a Mokwa da kewayenta.
- Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja
- Adadin Mutanen Da Suka Mutu Sanadin Ambaliya A Neja Ya Karu Zuwa 115
Sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Abubakar Usman a lokacin da yake mika wannan umarni, ya ce an dauki matakin ne a matsayin girmamawa ga wadanda lamarin ya rutsa da su da kuma ba da damar zaman makoki da addu’o’i a gare su.
Da yake mika umarnin Gwamnan ga Masarautun, Sakataren ya bayyana cewa, ambaliyar Mokwa na daya daga cikin mafi munin annoba da ta afku a jihar tsawon shekaru da dama da suka gabata, wacce ta yi sanadin salwantar rayuka da rugujewar gidaje da ababen more rayuwa da dama.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp