• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: Sanata Ahmed Lawan Ya Lashe Mazabarsa A Yobe Ta Arewa

by Muhammad Maitela
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Yanzu-yanzu: Sanata Ahmed Lawan Ya Lashe Mazabarsa A Yobe Ta Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Lawan ya lashe mazabarsa ta Arewacin Yobe da gagarumar nasara a zaben majalisun tarayya da na Shugaban kasa wanda ya gudana ranar Asabar a fadin kasar nan.

Da take sanar da sakamakon zaben da misalin 11:30 na daren ranar Lahadi, Baturiyar zaben (Returning Officer), Farfesa Omolola Aduloju, daga Jami’ar Gwamnatin Tarayya dake Gashu’a, a cibiyar tattarawa da sanar da sakamakon zaben kananan hukumomi shida (6) na Yobe ta Arewa; Bade, Jakusko, Karasuwa, Nguru, Yusufari da Machina, ta bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Sanata Ahmed Lawan a matsayin wanda ya samu nasara a zaben.

Ta kara da cewa, a cikin adadin kuri’un da aka yi rijista a kananan hukumomin, kimanin 122136, da yawan kuri’un da aka jefa a zaben 126677, sannan kuma da kuri’u 4541 da suka lalace; jam’iyyar NNPP ta samu kuri’u 7210, sai PDP mai kuri’u 22849, yayin da jam’iyyar APC ta samu adadin kuri’u 91318 a ilahirin kananan hukumomi shida a yankin.

Jami’ar zaben ta bayyana cewa, “Ni Farfesa Omolola, a matsayin Baturiyar zabe a Yobe ta Arewa, wanda ya gudana ranar 25 ga watan Fabarairun 2023, zabe ne da yan takara suka fafata. Kuma bisa dokar hukumar zabe mai zaman kanta (INEC), Sanata Ahmed Lawan na jam’iyyar APC shi ne dan takarar da ya zarta abokan takararsa da yawan kuri’u 91318, saboda haka na ayyana shi a matsayin wanda ya samu nasarar lashe zabe a Yobe ta Arewa.”

Kamar yadda sakamakon ya nuna, Sanata Lawan ya doke abokan takararsa na jam’iyyar PDP, Hon. Ilu Bello Yusufari, wanda ya samu kuri’u 22849, da kuma Hon. Daiyabu Garba Hamza na jam’iyyar NNPP mai kuri’u 7210, da Hon. Sheriff Alhaji Bunu na jam’iyyar ADC mai kuri’u 756.

Labarai Masu Nasaba

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Bugu da kari, an gudanar da zaben tare da sanar da sakamakon zaben a gaban wakilan yan takara da na jam’iyyu, jami’an tsaro da yan jaridu tare da masu sanya ido, cikin tsanaki da kwanciyar hankali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Sanata Abdul Ningi Ya Lashe Zaben Sanatan Bauchi Ta Tsakiya

Next Post

Yanzu-Yanzu: Dan Majalisar Dokokin Jihar Legas, Hon. Jimoh, Ya Rasu

Related

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

3 days ago
ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

5 days ago
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
Da ɗumi-ɗuminsa

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

6 days ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Da ɗumi-ɗuminsa

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

6 days ago
Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar

6 days ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Da ɗumi-ɗuminsa

Lauyoyin Majalisar Dattawa Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki

6 days ago
Next Post
Yanzu-Yanzu: Dan Majalisar Dokokin Jihar Legas, Hon. Jimoh, Ya Rasu

Yanzu-Yanzu: Dan Majalisar Dokokin Jihar Legas, Hon. Jimoh, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

July 13, 2025
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

July 13, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

July 13, 2025
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

July 13, 2025
Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.