ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: Sanata Ahmed Lawan Ya Lashe Mazabarsa A Yobe Ta Arewa

by Muhammad Maitela
3 years ago
Yobe

Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Lawan ya lashe mazabarsa ta Arewacin Yobe da gagarumar nasara a zaben majalisun tarayya da na Shugaban kasa wanda ya gudana ranar Asabar a fadin kasar nan.

Da take sanar da sakamakon zaben da misalin 11:30 na daren ranar Lahadi, Baturiyar zaben (Returning Officer), Farfesa Omolola Aduloju, daga Jami’ar Gwamnatin Tarayya dake Gashu’a, a cibiyar tattarawa da sanar da sakamakon zaben kananan hukumomi shida (6) na Yobe ta Arewa; Bade, Jakusko, Karasuwa, Nguru, Yusufari da Machina, ta bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Sanata Ahmed Lawan a matsayin wanda ya samu nasara a zaben.

Ta kara da cewa, a cikin adadin kuri’un da aka yi rijista a kananan hukumomin, kimanin 122136, da yawan kuri’un da aka jefa a zaben 126677, sannan kuma da kuri’u 4541 da suka lalace; jam’iyyar NNPP ta samu kuri’u 7210, sai PDP mai kuri’u 22849, yayin da jam’iyyar APC ta samu adadin kuri’u 91318 a ilahirin kananan hukumomi shida a yankin.

ADVERTISEMENT

Jami’ar zaben ta bayyana cewa, “Ni Farfesa Omolola, a matsayin Baturiyar zabe a Yobe ta Arewa, wanda ya gudana ranar 25 ga watan Fabarairun 2023, zabe ne da yan takara suka fafata. Kuma bisa dokar hukumar zabe mai zaman kanta (INEC), Sanata Ahmed Lawan na jam’iyyar APC shi ne dan takarar da ya zarta abokan takararsa da yawan kuri’u 91318, saboda haka na ayyana shi a matsayin wanda ya samu nasarar lashe zabe a Yobe ta Arewa.”

Kamar yadda sakamakon ya nuna, Sanata Lawan ya doke abokan takararsa na jam’iyyar PDP, Hon. Ilu Bello Yusufari, wanda ya samu kuri’u 22849, da kuma Hon. Daiyabu Garba Hamza na jam’iyyar NNPP mai kuri’u 7210, da Hon. Sheriff Alhaji Bunu na jam’iyyar ADC mai kuri’u 756.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Ibrahim Tanko Muhammad, Ya Rasu

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Yammacin Afirka

Bugu da kari, an gudanar da zaben tare da sanar da sakamakon zaben a gaban wakilan yan takara da na jam’iyyu, jami’an tsaro da yan jaridu tare da masu sanya ido, cikin tsanaki da kwanciyar hankali.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Ibrahim Tanko Muhammad, Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Ibrahim Tanko Muhammad, Ya Rasu

December 16, 2025
Juyin Mulki: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Yammacin Afirka
Da ɗumi-ɗuminsa

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Yammacin Afirka

December 9, 2025
An Tsare Sojojin Nijeriya 11 A Burkina Faso Bayan Jirginsu Ya Yi Saukar Gaggawa
Da ɗumi-ɗuminsa

An Tsare Sojojin Nijeriya 11 A Burkina Faso Bayan Jirginsu Ya Yi Saukar Gaggawa

December 9, 2025
Next Post
Yanzu-Yanzu: Dan Majalisar Dokokin Jihar Legas, Hon. Jimoh, Ya Rasu

Yanzu-Yanzu: Dan Majalisar Dokokin Jihar Legas, Hon. Jimoh, Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

December 22, 2025
Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.