Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, a ranar Talatar nan cikin dare ya ziyarci tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan a gidansa da ke gundumar Maitama a Abuja.
An ce ganawar dai na daga wani bangare na tuntubar masu ruwa da tsaki da neman shawarwari da Tinubun ke yi bisa rakiyar abokin takararsa Sanata Kashim Shettima da wasu Gwamnonin APC guda biyar, inda suka nemi goyon bayan tsohon shugaban kan zaben 2023 da ke tafe.
Kazalika dan takarar na amfani da irin wannan ziyarar wajen neman hanyoyin da zai tafiyar da kasar nan idan ya samu nasara a zaben 2023 da ke tafe.
Zuwa yanzu dai cikakken bayanin ganawar ta su bai fito fili ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp