Wasu ‘yan daba sun kashe wani dalibi mai matakin aji 300 na jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida da ke Lapai a jihar Neja, mai suna Jafar a safiyar ranar Litinin.
Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa, an kashe dalibin ne da misalin karfe 2:30 na dare a lokacin da ‘yan daban suka kai hari a Unguwar Ndakitabu a cikin garin Lapai.
- Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan
- Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
An caka wa marigayin wuka a wuya ne, inda aka garzaya da shi babban asibitin Lapai, inda daga bisani aka tabbatar da mutuwarsa.
Bayan faruwar lamarin ne, wasu fusatattun dalibai matasa suka tare hanyar Agaie-Lapai, suna nuna rashin amincewarsu da kisan da aka yi wa abokin su.
Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Neja, Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce, “Yau 23 ga watan Yuni, 2025 da misalin karfe 3 na dare, rundunar ta samu labarin cewa, da misalin karfe 2:30 na dare wasu ‘yan daba sun kai hari a wasu dakunan kwanan dalibai dake unguwar Ndakitabu ta Lapai, amma maharan sun tsere a lokacin da jami’an ‘yansandan suka isa wurin”.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp