• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yar Kasar Zambiya: A Nan Kasar Sin, Ina Jin Tamkar Ina Gida!

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Kasar Sin
0
Zambiya

‘Yar kasar Zambiya dake karatu a kasar Sin Charlette

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Saboda sha’awar da suke yi wa kasar Sin, wasu baki ‘yan kasashen waje sun shigo kasar. Domin neman cimma burinsu, wasu har sun zauna a kasar Sin, domin aiki, ko karatu. Mene ne ra’ayin baki ‘yan kasashen waje kan kasar Sin, musamman wadanda ke zaune a nan har na tsawon lokaci?

Kasar Sin da kasar Zambiya na da dadadden zumunci a tsakaninsu. A ranar 29 ga watan Oktoban shekara ta 1964, Zambiya ta kasance kasa ta farko dake yankin kudancin Afirka, wadda ta kulla huldar diflomasiyya da kasar Sin, kuma a shekarar da muke ciki wato 2024, aka cika shekaru 60 da kulla dangantakar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu. A halin yanzu, Sin da Zambiya na kara yin mu’amala da cudanya da juna ta fannoni daban-daban, har ma zumuncin al’ummunsu na dada inganta.

  • Kamfanonin Sin Sun Kara Kirkiro Sabbin Kayayyaki Masu Lambar Kira
  • Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Da Su Taimakawa Gwamnatocin Kasashe Masu Fama Da Rikici Wajen Tabbatar Da Rayuwar Yara A Dukkan Fannoni

‘Yan kasar Zambiya da dama sun san kasar Sin daga layin jirgin kasa da aka shimfida tsakanin Tanzaniya da Zambiya, wanda kasar Sin ta taimaka wajen ginawa lokacin da ita ma take fama da talauci. Kawo yanzu kusan rabin karni ya wuce, amma layin jirgin kasan na ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen karfafa sada zumunta tsakanin al’ummun Sin da Afirka, musamman na Tanzaniya da Zambiya.

Charlette, daya ce daga cikin ‘yan kasar Zambiya da suka fara sanin labarin kasar Sin daga hanyar jirgin kasa tsakanin kasashen Tanzaniya da Zambiya, wanda ke shaida zumunci mai karfi tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka. Bayan shigowarta kasar Sin zuwa yanzu, Charlette ta kara fahimtar kasar Sin, wadda ke da ci gaban kimiyya da fasaha, da mabambantan wayin kai, da al’umma masu karamci sosai.

“A ganina, mutanen kasar Sin na da kirki da son karbar baki. A nan kasar Sin, ina jin tamkar ina gida Zambiya. Ba na kewar gida sosai, saboda nan tamkar gidana ne.”

Labarai Masu Nasaba

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

Zambiya
Fasinjoji na cikin jirgin kasa dake zirga-zirga tsakanin Tanzaniya da Zambiya

Charlette ta sha bayyana cewa kasar Sin tamkar gida yake a wajenta. Kafin ta shigo kasar, tana shakku kan rayuwa da karatu a kasar Sin. Amma iyayenta sun karfafa mata gwiwa gami da ba ta cikakken goyon-baya. A lokacin kuruciyarta, Charlette da mahaifiyarta sun taba ziyartar ‘yan uwansu a Tanzaniya ta hanyar jirgin kasa tsakanin Tanzaniya da Zambiya. Kana, a ‘yan shekarun nan, mahaifin Charlette ya sha zuwa aiki kasar Sin, da ba ta labarin da ya shafi kasar. Har ma mijin babarta dan China, ya ba ta shawarar kara ilimi a kasar Sin. Charlette ta ce:

“Ya ce akwai ci gaban fasahohi sosai a kasar Sin, kuma karatu a kasar zai ba ni karin damarmakin fahimtar al’adun kasar. Shi ma mahaifina ya taba bayyana min labarin ziyararsa a kasar Sin, inda ya ce, ana amfani da wayar salula wajen biyan kudin sayayya a kasar, mutane kadan ne ke amfani da takardun kudi, al’amuran da suka ba ni sha’awa sosai.”

A shekara ta 2019, Charlette ta fara karatu a jami’ar Huaqiao dake birnin Xiamen na lardin Fujian dake kasar Sin. A farkon zuwanta, ta yi iyakacin kokarinta wajen karatun harshen Sinanci, amma tana fuskantar wasu matsaloli, kamar rashin haduwa da iyali da ‘yan uwa da abokai na gida, da rashin gane harshen Sinanci sosai da sauransu. Da take waiwayen farkon zuwanta kasar Sin, Charlette ta ce, ta gode wa malamai da abokan karatunta na kasar Sin sosai, wadanda a cewarta, suka samar mata da cikakken goyon-baya da matukar kulawa, al’amarin da ya taimaka mata sosai wajen haye wahalhalu. Charlette ta ce:

Zambiya
Charlette(ta uku daga hannun dama) tare da sauran wasu daliban kasashen waje dake karatu a jami’ar Huaqiao

“Na fuskanci kalubale a farkon zuwana kasar Sin. Ni mutumiya ce mai jin kunya, amma malamai da abokan karatuna sun taimake ni sosai, musamman abokan karatuna na kasar Sin. A wani lokaci, na kan yi kuskure yayin da nake magana da Sinanci, amma su kan ba ni hakuri, da koya min yadda zan yi magana daidai. Koyon harshen Sinanci, abu ne mai ban sha’awa, amma kuma mai wahalar gaske. Yanzu zan iya cewa na riga na shawo kan matsalolin.”

A halin yanzu, Charlette tana karatun digiri na farko a tsangayar koyon ilimin injuna masu kwakwalwa dake jami’ar Huaqiao, kuma tana da wani suna na harshen Sinanci, da ake kira Li Yixin. Charlette ta riga ta saba da rayuwa a birnin na Xiamen, inda take jin dadin kyakkyawan yanayin wajen. Charlette ta ce:

“Xiamen, birni ne mai ni’ima da kuma kyan-gani, kuma abincin wurin na da dadi kuma ya dace da ni. Ni ba na son abinci mai yaji. A ganina, Xiamen birni ne mai jan ra’ayin baki ta fannoni daban-daban, farashin kayayyaki na da sauki, haka kuma rayuwa tana da dadi. Ke nan, birni ne mai kyau sosai.”

Charlette ta ce, Sin hamshakiyar kasa ce, kuma tana fatan ziyartar wurare daban-daban a kasar, don ganewa idanunta mabambantan al’adu da yanayin rayuwa a kasar. Charlette ta ce, ban da Xiamen, birni na daban da ya burge ta shi ne Shanghai, inda ta ce:

“Dalilin da ya sa na je Shanghai shi ne, domin abokaina sun ba ni shawarar zuwa sau da dama. Shanghai na da kyan-gani sosai! Na ziyarci husumiyar TV da ake kira Oriental Pearl, da babban ginin Shanghai Tower, wuraren da dama na taba ganinsu a shirin talabijin, amma yanzu na gani a zahiri, kuma gani ya kori ji. Ina matukar farin-ciki.”

Zambiya
Daliban kasar Angola dake karatu a jami’ar Huaqiao na gabatar da wasan gargajiya na kasar Sin

Kasar Sin da kasar Zambiya, aminan juna ne masu zumunci sosai a tsakaninsu. Charlette ta ce, kullum ta kan samu labaran mu’amala da hadin-gwiwa tsakanin kasashen biyu, kuma tana fatan zumuncinsu zai kara inganta. Ta ce:

“A karkashin jagorancin shawarar ‘ziri daya da hanya daya’, Sin ta taimaki Zambiya a bangarori daban-daban, ciki har da gina hanyoyin mota, da filayen jiragen sama, da zuba jari a aikin noma da sana’ar kere-kere da sauransu. Duk wadannan ayyukan da kasar Sin ta yi a Zambiya, sun taimaka sosai ga ci gaban tattalin arzikin kasarmu. Kaza lika, na san akwai daliban Zambiya da yawa da a yanzu haka suke kara ilimi a kasar Sin, kuma irin wannan mu’amalar ilimi za ta kara samar da fahimtar juna tsakanin kasashen biyu. Babban abun da nake fatan gani shi ne, Zambiya za ta kara koyon fasahohin zamani daga kasar Sin, musamman a halin yanzu ana sayar da hajojin kasar Sin a duk fadin duniya, ya dace Zambiya ta yi koyi a wannan fanni.”

Asalin Charlette yana Ndola, birni mafi gima na uku a kasar Zambiya, kana birnin da ya shahara sosai a fannin masana’antu. Charlette ta kara da cewa, yin karatu a kasar Sin, zabi ne mafi dacewa da ta yi, ganin yadda kasar take da saurin ci gaba a fannonin tattalin arziki da zaman rayuwar al’umma, kuma akwai abubuwan da ya kamata kasashen Afirka su koya. Game da burinta a nan gaba, Charlette ta ce, tana fatan za ta koma Zambiya tare da ilimi da fasahohin da ta samu a kasar Sin, don bada gudummawa ga gina kasarta, inda ta ce:

“Ina jin dadin rayuwa a kasar Sin, wani sabon salon rayuwa ne a gare ni. Haka kuma na koyi abubuwa da yawa a nan. Ina fatan zan iya kammala karatu yadda ya kamata a kasar Sin, in koma gida Zambiya tare da ilimi da fasahohin da na koya a nan.”

Kamar ita Charlette, akwai dalibai ‘yan kasashen Afirka da dama, wadanda ke karatu a jami’ar Huaqiao dake birnin Xiamen na lardin Fujian dake kasar Sin, ciki har da Zambiya, Angola, Madagascar, Mauritius, Sudan da sauransu. Kuma har yanzu daliban Afirka da suka gama karatu a jami’ar, suna gudanar da ayyukan da suka shafi kasuwanci tsakanin Sin da Afirka, da mu’amalar al’adu tsakaninsu.

Zambiya
Wasu daliban kasashen waje dake karatu a jami’ar Huaqiao

Ilimi, daya ne daga cikin fannonin hadin-gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka. Ban da wannan, kwalliya ta biya kudin sabulu wajen karfafa hadin-gwiwar Sin da Afirka a sauran wasu fannoni da dama. Alal misali, Sin ta zama aminiyar cinikayya mafi girma ga Afirka har na tsawon shekaru 15, kana, Sin kasa ce mai tasowa mafi girma da ta zuba wa Afirka jari. Sa’annan a fannin neman zamanantarwa, har kullum kasar Sin ta kan marawa kasashen Afirka baya wajen zamanantar da kansu. A wajen shawarwarin shugabannin Sin da Afirka da aka gudanar a watan Agustan shekara ta 2023, kasar Sin ta bullo da shawarar goya wa Afirka baya wajen raya sana’o’i, da yin alkawarin karfafawa kamfanoninta gwiwa don su baiwa Afirka taimakon raya sana’ar kere-kere, da habaka tattalin arzikinsu ta fannoni daban-daban. Kaza lika, Sin ta yi alkawarin aiwatar da “shirin taimakawa Afirka zamanantar da sana’ar noma”, don kara zuba jari ga sana’ar noma ta Afirka, da fadada hadin-gwiwar Sin da Afirka ta fuskar kimiyya da fasahar aikin gona, da kokarin kawo sauye-sauye ga sana’ar noma ta Afirka. A dayan bangaren kuma, kasar Sin ta sanar da “shirin hadin-gwiwa na horas da kwararru”, don inganta kwarewar kasashen Afirka ta fuskar raya kansu.

Zambiya
Charlette(ta uku daga hannun dama) tare da sauran wasu daliban kasashen waje dake karatu a jami’ar Huaqiao

Muna iya ganin cewa, Sin da Afirka za su kara cimma nasarori a hadin-gwiwa da mu’amalarsu a nan gaba, don kara samar da alfanu da alheri ga daukacin al’ummunsu baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata Da Laraba A Matsayin Ranakun Hutun Sallar Eid-el-Fitr 

Next Post

Jakadan Sin A Amurka: Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko Ya Inganta Ci Gaban Sin Da Duniya

Related

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya
Daga Kasar Sin

Bude Kasar Sin Na Kyautata Ci Gaban Duniya

2 months ago
Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin
Daga Kasar Sin

Mu Leka Jihar Mongolia Ta Gida Dake Arewacin Kasar Sin

10 months ago
wang lili
Daga Kasar Sin

Yadda Wang Lili Ke Kiyaye Neman Cimma Nasara A Wasan Kwallon Kwando

10 months ago
Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura
Daga Kasar Sin

Kumbon Sin Ya Tashi Daga Bangaren Duniyar Wata Mai Nisa Dauke Samfura

11 months ago
Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin
Daga Kasar Sin

Ba Shakka Kamfanonin Ketare Za Su Ci Riba In Suka Zuba Jari Da Aiwatar Da Ayyukansu A Sin

1 year ago
Salon Dimokuradiyya Mai Sigar Musamman Ta Kasar Sin 
Daga Kasar Sin

Salon Dimokuradiyya Mai Sigar Musamman Ta Kasar Sin 

1 year ago
Next Post
Jakadan Sin A Amurka: Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko Ya Inganta Ci Gaban Sin Da Duniya

Jakadan Sin A Amurka: Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko Ya Inganta Ci Gaban Sin Da Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.