• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

by Sani Anwar and Sulaiman
1 month ago
A health worker administers a cervical cancer vaccine HPV Gardasil to a girl on the street in Ibadan, Nigeria, on May 27, 2024. African countries have some of the world's highest rates of cervical cancer. Growing efforts to vaccinate more young girls for the human papillomavirus are challenged by the kind of vaccine hesitancy seen for some other diseases. Misinformation can include mistaken rumors that girls won't be able to have children in the future. Some religious communities must be told that the vaccine is "not ungodly." More than half of Africa's 54 nations – 28 – have introduced the vaccine in their immunization programs, but only five have reached the 90% coverage that the continent hopes to achieve by 2030. (AP Photo/Sunday Alamba)

A health worker administers a cervical cancer vaccine HPV Gardasil to a girl on the street in Ibadan, Nigeria, on May 27, 2024. African countries have some of the world's highest rates of cervical cancer. Growing efforts to vaccinate more young girls for the human papillomavirus are challenged by the kind of vaccine hesitancy seen for some other diseases. Misinformation can include mistaken rumors that girls won't be able to have children in the future. Some religious communities must be told that the vaccine is "not ungodly." More than half of Africa's 54 nations – 28 – have introduced the vaccine in their immunization programs, but only five have reached the 90% coverage that the continent hopes to achieve by 2030. (AP Photo/Sunday Alamba)

Yayin da duniya ke bikin watan wayar da kan yara kananan, Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta bayyana cewa; akalla yara 400,000ne ke kamuwa da cutar kansa a duk shekara a duniya, kwatankwacin yara uku a duk minti hudu.

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), ta lura da yadda ake samun banbanci a tsakanin masu dauke da cutar, domin kuwa kashi 80 cikin 100 na yara a cikin kasashe masu tasowa, suna tsira daga cutar kansar, idan aka kwatanta da daya cikin biyar na matalautan kasashe da kuma tsaka-tsaki. Hukumar ta bayyana wannan a matsayin “daya daga cikin mafi girman rashin daidaito a bangaren da shafi cutar kansar.”

Da yake magana a wani taron masu ruwa da tsaki na yara kanana a Masar, wadanda suka tsira sun bayyana yadda suka sha fama da cutar. Daya daga cikin wadanda suka tsiran, ya bayyana wa mahalarta taron cewa; “Cutar ta yi yunkurin hallaka ni, amma taimakon likitoci da dangina da kuma abokaina ne ya karfafe ni. Ga shi a yau ina karar da labarina, ni da kaina.”

Taron, wanda Ministan Lafiya na Kasar Dakta Khaled Abdel-Ghaffar ya kaddamar, ya hada da kwararru da wadanda suka tsira da ransu, wadanda suka yi kira da a dauki matakan gaggawa, domin tseratar da rayuka.

A shekarar 2018, Hukumar Lafiya ta Duniya da Cibiyar Nazarin yara, sun kaddamar da kungiyar GICC da manufar habaka ceto rayukan yara kanana da kashi 60 cikin 100 daga nan zuwa 2030. Duk da kalubale irin daban-daban da suka shafi rikice-rikice da karancin lafiya, ana samun ci gaba a kasashe da dama karkashin tsarin kulawar Hukumar Lafiya ta Duniya.

LABARAI MASU NASABA

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Kasashe takwas, ciki har da Pakistan, Morocco, Syriya, Libya, Jordan, Lebanon da kuma Masar, sun himmatu wajen bayar da fifikon kula da cutar kansa ta yara, ta hanyar kula da ka’idojin kasa, ta hanyar yin gwajin cutar da a kan lokaci, samar da ingantattun magunguna da kuma samar da kudade don bai wa iyali kariya.

Kwanan nan, Maroko ta karbi bakuncin taron bita na farko, kan kula da lafiyar yara, yayin da Lebenon kuma ta kafa kwamitin kula da cutar kansar yara, wanda ya shafi wadanda suka tsira da rayukansu, ma’aikatan jinya, sauran ma’aikata da kuma wakilan Hukumar Kula da Lafiya ta Duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC
Labarai

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Manyan Labarai

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Next Post
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

LABARAI MASU NASABA

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025
Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

October 19, 2025
Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.